< 2 Samuel 16 >
1 David s'était à peine éloigné de Rhos, quand arriva, devant lui, Siba, le serviteur de Miphiboseth, avec deux ânes chargés; or, il y avait sur les ânes deux cents pains, cent sacs de raisins secs, cent sacs de dattes et un nébel de vin.
Sa’ad da Dawuda ya yi ɗan nesa da ƙwanƙolin, sai ga Ziba mai hidimar Mefiboshet, yana jira yă tarye shi. Yana da jerin jakuna da sirdi suna ɗauke da dunƙulen burodi ɗari biyu, da ƙosai busasshen inabi ɗari ɗaya, da kosan’ya’yan itace ɓaure guda ɗari, da salka ruwan inabi.
2 Et le roi dit à Siba: Que veux-tu faire de cela? Siba répondit: Les bêtes sont à la famille du roi, pour qu'elle les monte; les pains et les dalles, aux jeunes serviteurs, pour qu'ils les mangent; le vin, à ceux qui tomberont de fatigue dans le désert, pour qu'ils le boivent.
Sarki ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo waɗannan?” Ziba ya ce, “Jakuna domin iyalin gidan sarki su hau ne, burodi da’ya’yan itace domin mutane su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suka gaji a hamada.”
3 David reprit: Où est le fils de ton maître? Et Siba répondit: Il est resté à Jérusalem, parce qu'il a dit: Aujourd'hui la maison d'Israël va me rendre la royauté de mon père.
Sai sarki ya ce, “Ina jikar maigidanka?” Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima gama yana tsammani cewa, ‘Yau gidan Isra’ila za su mayar mini da sarautar kakana.’”
4 Et le roi dit à Siba: Tout ce qui appartenait à Miphiboseth est à toi; et Siba, se prosternant, lui répondit: Puissé-je avoir trouvé grâce à tes yeux, ô roi, mon maître.
Sai sarki ya ce wa Ziba, “Duk abin da yake na Mefiboshet, ya zama naka.” Ziba ya rusuna ya ce, “Bari in dinga samun tagomashi a gabanka ranka yă daɗe.”
5 Et le roi David alla jusqu'à Bathurim, et il sortit de là un homme de la famille de Saül, nommé Sémeï, fils de Géra; il sortit; et, en marchant, il maudissait David;
Yayinda Sarki Dawuda ya kusato Bahurim, sai ga wani mutumin dangin Shawulu ya fito daga can, sunansa Shimeyi ɗan Gera. Ya fito yana ta la’anta yayinda yake fitowa.
6 Il jetait des pierres au roi et à tous ses serviteurs. Or, tout le peuple était là avec tous les hommes vaillants, les uns à droite, les autres à la gauche du roi.
Ya jajjefi Dawuda da dukan fadawan sarki da duwatsu, ko da yake sojoji da masu gadin sarki na musamman suna kewaye da sarki dama da hagu.
7 Sémeï maudissait donc, disant: Hors d'ici, hors d'ici, homme de sang, homme de péché!
Yayinda yake la’antar, Shimeyi ya ce, “Tafi daga nan, tafi daga nan, mai kisankai, mutumin banza kawai!
8 Le Seigneur a fait retomber sur toi tout le sang de la maison de Saül, après que tu as régné à sa place. Et le Seigneur a donné ton royaume à ton fils Absalon; te voilà pris dans ta propre méchanceté, parce que tu es un homme de sang.
Ubangiji ya kama ka saboda alhakin jinin gidan Shawulu, wanda kake sarauta a maimakonsa. Ubangiji ya ba da masarautar ga ɗanka Absalom. Hallaka ta zo maka domin kai mai kisankai ne!”
9 Abessa, fils de Sarvia, dit à David: Pourquoi ce chien mort maudit-il le roi mon maître? Je vais à lui, et je lui trancherai la tête.
Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce wa sarki, “Ranka yă daɗe, don me wannan mataccen kare yake la’antarka? Bari in je in datse kansa.”
10 Mais le roi répondit: Qu'y a-t-il entre vous et moi, fils de Sarvia? Laisse-le, et qu'il continue de maudire, car le Seigneur lui a dit de maudire David; qui donc ira lui dire: D'où vient que tu agis de la sorte?
Amma sarki ya ce, “Ba ruwana da ku, ku’ya’yan Zeruhiya. Idan yana la’ana ne domin Ubangiji ya ce masa, ‘La’anci Dawuda,’ wa zai ce, ‘Don me kake haka?’”
11 David dit encore à Abessa et à tous ses serviteurs: Voilà que mon fils, sorti de mes entrailles, en veut à ma vie, et en outre vous entendez maintenant ce fils de Benjamin; laissez-le maudire, car le Seigneur le lui a dit.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Abishai da dukan fadawansa, “Ɗana, na cikina, yana ƙoƙari yă kashe ni. Balle wannan mutumin Benyamin! Ku ƙyale shi, yă yi ta zargi, Ubangiji ne ya ce masa yă yi haka.
12 S'il advient que le Seigneur jette un regard sur mon humiliation, il me rendra ses bienfaits pour prix des malédictions de cet homme.
Mai yiwuwa Ubangiji yă ga azabata, yă sāka mini da alheri saboda la’anar da nake sha a yau.”
13 Et David continua de suivre la route avec tous les siens; et Seine, sur les flancs de la montagne, s'attachant à ses pas, continua de le maudire, de lui jeter des pierres, et de faire voler sur lui la poussière du chemin.
Saboda haka Dawuda da mutanensa suka ci gaba da tafiyarsu yayinda Shimeyi yana tafiya ɗaura da shi a gefen tudu, yana zagi, yana jifansa da duwatsu, yana tayar masa da ƙura.
14 Le roi et tout le peuple qui l'accompagnait arrivèrent à Bathurim exténués de fatigue; ils y reprirent haleine.
Sarki da dukan mutanen da suke tare da shi suka isa masauƙinsu a gajiye. A can fa ya huta.
15 Absalon venait donc d'entrer à Jérusalem, et avec lui tous les hommes d'Israël, et Achitophel.
Ana cikin haka, Absalom da dukan Isra’ila suka iso Urushalima, Ahitofel kuwa yana tare da shi.
16 Quand Chusaï, le favori de David, alla trouver Absalon, et lui dit: Vive le roi!
Sai Hushai mutumin Arkitawa, abokin Dawuda ya je wurin Absalom ya ce masa, “Ran sarki yă daɗe! Ran sarki yă daɗe!”
17 Absalon dit à Chusaï: Voilà comme tu as compassion de ton ami? Pourquoi n'es-tu pas parti avec ton ami?
Absalom ya ce wa Hushai, “Ƙaunar da kake nuna wa abokinka ke nan? Me ya sa ba ka tafi tare da abokinka ba?”
18 Dieu m'en garde, reprit Chusaï; je suivrai celui qu'ont choisi le Seigneur, et tout le peuple et tout Israël; je serai à lui, je résiderai où il résidera.
Hushai ya ce wa Absalom, “A’a, ai, wanda Ubangiji ya zaɓa ta wurin waɗannan mutane, da kuma ta wurin dukan mutane Isra’ila, shi zan zama nasa, zan kuma kasance tare da shi.
19 Et, encore une fois, qui donc servirais-je, si ce n'est le fils de mon maître? Comme j'ai servi ton père, je te servirai.
Ban da haka ma, wane ne zan bauta wa? Ashe, ba ɗan ne zan bauta wa ba? Kamar dai yadda na bauta wa mahaifinka, haka zan bauta maka.”
20 Absalon dit ensuite à Achitophel: Délibérez entre vous sur ce que nous ferons.
Absalom ya ce wa Ahitofel, “Ba mu shawararka. Me za mu yi?”
21 Et Achitophel dit à Absalon: Approche-toi des concubines de ton père, qu'il a laissées pour garder son palais; tout Israël apprendra que tu as déshonoré ton père, et les mains de ceux de ton parti seront fortifiées.
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Je ka kwana da ƙwarƙwaran mahaifinka waɗanda ya bari su lura da fada. Ta haka dukan Isra’ila za su ji cewa ka mai da kanka abin wari a hancin mahaifinka, dukan hannuwan waɗanda suke tare da kai kuwa za su sami ƙarfi.”
22 Puis, ils dressèrent une tente sur la plate-forme du palais, et Absalon s'approcha des concubines de son père aux yeux de tout Israël.
Saboda haka suka kafa wa Absalom tenti a bisa rufin ɗaki, a can ya kwana da ƙwarƙwaran mahaifinsa a gaban dukan Isra’ila.
23 Les conseils que donnait Achitophel, en ces premiers jours, étaient reçus comme ceux d'un homme qui aurait consulté Dieu. Ainsi pensaient de tout conseil d'Achitophel David aussi bien qu'Absalon.
To, a kwanakin nan shawarar da Ahitofel yakan bayar takan zama kamar wadda aka nemi daga Allah ne. Haka Dawuda da Absalom duk suke ɗaukan dukan shawarar Ahitofel.