< 2 Rois 24 >

1 En ce temps-là, Nabuchodonosor, roi de Babylone, vint, et Joacin lui fut asservi trois ans; ensuite il changea de pensée, et il refusa de lui obéir.
A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
2 Alors, le Seigneur envoya contre lui des bandes de la Chaldée, de la Syrie, de Moab et des fils d'Ammon; il les envoya en la terre de Juda pour prévaloir sur elle, selon la parole que le Seigneur avait dite par la voix de ses serviteurs les prophètes;
Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
3 De plus, la colère du Seigneur contre Juda voulait l'expulser de devant sa face à cause des péchés de Manassé, et de tout ce qu'avait fait ce roi;
Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
4 Car il avait versé le sang innocent, il en avait rempli Jérusalem; et le Seigneur ne voulait point s'apaiser.
haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
5 Quant au reste de l'histoire de Joacin, n'est-il pas écrit au livre des Faits et gestes des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
6 Et Joacin s'endormit avec ses pères, et son fils Joachim, régna à sa place.
Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
7 Et le roi d'Égypte ne sortit plus de sa contrée, parce que, depuis le torrent d'Égypte jusqu'à l'Euphrate, le roi de Babylone avait pris tout ce qui appartenait à l'Égyptien.
Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
8 Joachim avait dix-huit ans quand il monta sur le trône, et il régna trois mois à Jérusalem; sa mère se nommait Nestha, fille d'Ellanastham, de Jérusalem.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
9 Et il fit le mal devant le Seigneur, comme avait fait son père.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
10 En ce temps-là, Nabuchodonosor, roi de Babylone, marcha sur Jérusalem, et la ville fut investie.
A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
11 Et Nabuchodonosor mit le siège devant la ville, et ses serviteurs la tinrent assiégée.
Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
12 Or, Joachim, roi de Juda, se rendit au roi de Babylone, lui, ses serviteurs, sa mère, ses chefs et ses eunuques; le roi de Babylone le fit captif en la huitième année de son règne.
Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
13 Et il enleva de Jérusalem tous les trésors du temple du Seigneur et tous les trésors du palais du roi; il brisa tous les vaisseaux d'or qu'avait faits, dans le temple, le roi Salomon, selon la parole du Seigneur.
Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
14 Et il emmena en captivité, au nombre de dix mille, tous les chefs, tous les hommes vaillants, et en outre tous les charpentiers et tous les maçons; il ne resta dans la terre que les indigents.
Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
15 Il transporta aussi à Babylone, Joachim, la mère du roi, les femmes du roi et ses eunuques; il conduisit tous les riches de la terre de Jérusalem à Babylone,
Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
16 Et tous les hommes dans la force de l'âge au nombre de soixante-dix mille, et mille charpentiers ou maçons, tous faisant la guerre. Le roi Nabuchodonosor les emmena captifs à Babylone.
Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
17 Et il remplaça Joachim par Batthanias, fils de Josias, et il donna à ce roi le nom de Sédécias.
Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
18 Sédécias avait vingt-neuf ans quand il monta sur le trône, et il régna onze ans à Jérusalem; le nom de sa mère était Amital, fille de Jérémie.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
19 Et il fit le mal devant le Seigneur, comme avait fait Joacin;
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
20 Car, telle était la pensée du Seigneur contre Jérusalem et contre Juda, jusqu'à ce qu'il les eut expulsés de devant sa face. Or, Sédécias se révolta contre le roi de Babylone.
Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.

< 2 Rois 24 >