< 2 Rois 18 >

1 En la troisième année du règne d'Osée, en Israël, Ezéchias, fils d'Achaz, devint roi de Juda.
A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Il avait vingt-cinq ans quand il monta sur le trône, et il régna vingt- neuf ans à Jérusalem; sa mère se nommait Abu, fille de Zacharie.
Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
3 Et il fit ce qui est droit aux yeux du Seigneur, se conformant à tout ce qu'avait fait David, son aïeul.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
4 Ce fut lui qui détruisit les hauts lieux, qui abattit les colonnes, qui arracha les bois sacrés, et le serpent d'airain qu'avait fait Moïse; car, jusqu'à ces jours-là, les enfants d'Israël l'avaient encensé; Ezéchias lui donna le nom de Neesthan.
Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
5 En Dieu seul il mit son espérance, et après lui il n'y eut point en Juda de roi qui lui ressemblât, et il n'y en avait pas eu parmi ceux qui l'avaient précédé.
Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
6 Il s'attacha au Seigneur, et il ne cessa pas de le suivre; il observa tous les commandements qu'il avait donnés à Moïse.
Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
7 Et le Seigneur était avec lui, et il montra de la sagesse en toutes ses entreprises; il se révolta contre le roi des Assyriens, et il ne lui resta pas asservi.
Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
8 Ce fut lui qui frappa les Philistins jusqu'à Gaza et sa banlieue, depuis les tours des guetteurs jusqu'aux cités fortifiées.
Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
9 En la quatrième année du règne d'Ezéchias (la septième année du règne d'Osée, en Israël), Salmanasar, roi des Assyriens, ayant marché contre Samarie, l'assiégea.
A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
10 Et il la prit au bout de trois ans, en la huitième année du règne d'Ezéchias (la neuvième du règne d'Osée, celle où tomba Samarie).
A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
11 Puis, le roi des Assyriens transporta ses habitants en Haba et en Habor, sur le fleuve Gozan, et sur les montagnes des Mèdes;
Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
12 Parce que les Samaritains n'avaient point obéi à la voix du Seigneur, qu'ils avaient violé son alliance, qu'ils n'avaient ni écouté, ni pratiqué ce qu'il avait prescrit à son serviteur Moïse.
Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
13 En la quatorzième année du règne d'Ezéchias, Sennachérib, roi des Assyriens, vint assiéger les villes fortes de Juda, et il les prit.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
14 Alors, le roi Ezéchias envoya des messagers au roi des Assyriens à Lachis, disant: J'ai failli, éloigne-toi de moi; ce dont tu me chargeras, je le porterai. Et le roi des Assyriens chargea Ezéchias d'une taxe de trois cents talents d'argent et trois cents talents d'or.
Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
15 Et le roi de Juda donna tout l'argent qui se trouva dans le temple et dans les trésors de son palais.
Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
16 En ce temps-là, Ezéchias ôta l'or des portes du temple et les lames d'or dont il avait lui-même revêtu les colonnes, et il les donna au roi des Assyriens.
A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
17 Et le roi des Assyriens envoya de Lachis, au roi Ezéchias, Tharthan, Rhaphis et Rhabsacès, accompagnés d'une forte armée; ils arrivèrent devant Jérusalem, et s'arrêtèrent à l'aqueduc de la piscine supérieure qui est sur le chemin du Champ du Foulon.
Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
18 De là, ils appelèrent à grands cris Ezéchias; aussitôt Eliacim, fils d'Helcias, l'économe; Sobna le scribe, et Joas, fils de Saphat, l'archiviste, vinrent les trouver.
Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
19 Et Rhabsacès leur dit: Dites à Ezéchias: Voici ce que dit le grand roi, le roi des Assyriens: Quel est l'appui en qui tu t'es confié?
Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
20 Tu as dit (mais seulement des lèvres): Mon conseil, mon armée, inclinent pour la guerre; maintenant donc, en qui t'es-tu confié, pour te révolter contre nous?
Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
21 Voyons, n'as-tu point foi en ce roseau brisé qu'on appelle l'Égypte? Il entrera dans la main de quiconque s'appuiera sur lui, et il la percera. Voilà comment est le Pharaon d'Égypte pour tous ceux qui se fient en lui.
Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
22 Mais, tu m'as dit: Nous nous confions en Dieu le Seigneur. Or, ce Dieu n'est-il pas le même dont Ézéchias a détruit, sur les hauts lieux, les autels, quand il a donné cet ordre à Jérusalem et à Juda: Vous adorerez, devant cet autel seul, dans Jérusalem?
Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
23 Eh bien! combats aujourd'hui mon maître le roi des Assyriens, et je te donnerai deux mille chevaux, si tu peux te donner toi-même deux mille cavaliers.
“‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
24 Comment donc feras-tu reculer le moindre des chefs qui servent mon maître? Et tu mets ta confiance en l'Égypte, en ses chars, en ses chevaux!
Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
25 Est-ce que nous sommes venus détruire cette terre sans le Seigneur? Le Seigneur m'a dit: Marche sur cette terre, et détruis-la.
Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
26 Et Eliacim, fils d'Helcias, Sobna et Joas dirent à Rhabsacès: Parle syrien à tes serviteurs, car nous l'entendons; ne nous parle pas en langue judaïque. Pourquoi parles-tu pour être ouï du peuple qui est sur les remparts?
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
27 Mais Rhabsacès répondit: Est-ce que mon maître m'a envoyé dire ces paroles à ton maître et à toi? Ne sont-elles pas pour les hommes qui se tiennent sur les remparts, et qui sont réduits comme vous à manger leurs excréments et à boire leur urine?
Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
28 Et Rbabsacès, se redressant, éleva la voix, et dit en langue judaïque: Écoutez les paroles du grand roi des Assyriens;
Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
29 Voici ce que dit le roi: Qu'Ezéchias ne vous excite point par ses discours, car il ne pourra vous arracher de mes mains.
Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
30 Qu'Ézéchias ne vous fasse point espérer au Seigneur, disant: Le Seigneur nous délivrera; il ne livrera point sa ville au roi des Assyriens.
Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
31 N'écoutez point Ezéchias; car voici ce que dit le roi des Assyriens: Cherchez auprès de moi votre bénédiction; venez à moi, et chacun boira le vin de sa vigne, chacun mangera les fruits de son figuier, chacun boira l'eau de sa citerne,
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
32 Jusqu'à ce que je revienne pour vous transporter en une terre comme la vôtre, en une terre de blé et de vignes, terre de pain et de vin, terre d'huile et de miel; et vous vivrez et vous ne mourrez point. N'écoutez point Ezéchias; car il vous trompe, quand il dit: Le Seigneur vous délivrera.
har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
33 Les dieux des nations qui tour à tour sont tombées dans les mains du roi, les ont-ils délivrées?
Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
34 Où est le dieu d'Emath et d'Arphad? Où est le dieu de Sepharvaïm, d'Ana et d'Abe? Ont-ils délivré Samarie de mes mains?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
35 Quel est donc celui des dieux, de toutes les nations, qui ait délivré sa terre de mes mains? Le Seigneur délivrera-t-il Jérusalem de mes mains?
Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
36 Et le peuple resta muet; personne ne répondit à ce discours; car le roi l'avait ainsi ordonné, disant: Ne lui répondez pas.
Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
37 Et l'économe Eliacim, fils d'Helcias, le scribe Sobna et l'archiviste Joas, fils de Saphat, rentrèrent auprès d'Ezéchias après avoir déchiré leurs vêtements; ils lui rapportèrent les paroles de Rhabsacès.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.

< 2 Rois 18 >