< 2 Chroniques 34 >

1 Josias avait huit ans quand il monta sur le trône, et il régna trente et un ans à Jérusalem.
Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
2 Il fit ce que est droit devant le Seigneur, et il marcha dans les voies de David, son aïeul; il ne s'en écarta ni à droite ni à gauche.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
3 Et, dans la huitième année de son règne, il était encore un adolescent quand il commença à chercher le Seigneur Dieu de David; et, dans la douzième année, il se mit à purifier Juda et Jérusalem des hauts lieux, des bois sacrés, des ornements des autels et des idoles jetées en fonte.
A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
4 Et il renversa, de devant sa face, les autels de Baal et, au-dessus d'eux, les hauts lieux; il abattit les bois sacrés et les statues; il brisa les idoles jetées en fonte, il les réduisit en poudre, et les jeta sur la surface des tombeaux de ceux qui leur avaient sacrifié.
A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
5 Et il brûla les ossements de leurs prêtres sur les autels; et il purifia Jérusalem et Juda,
Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
6 Puis, les villes de Manassé, d'Ephraïm, de Siméon et de Nephthali, et les bourgs qui les environnaient.
Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
7 Et il détruisit les autels et les bois sacrés, et il réduisit en poudre les idoles, et il renversa tous les hauts lieux d'Israël, et il revint à Jérusalem.
ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
8 Dans la dix-huitième année de son règne, après avoir purifié la terre et son palais, il envoya Saphan, fils d'Ezélias, Maasa, chef de la ville, et Juach, fils de Joachaz, son secrétaire-archiviste, pour réparer le temple du Seigneur son Dieu.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
9 Il se rendirent auprès d'Helcias, le grand prêtre, et ils lui donnèrent l'argent offert au temple de Dieu, recueilli, par les lévites gardiens de la porte, des mains de Manassé, d'Ephraïm, des princes, de tout le reste d'Israël, des fils de Juda et de Benjamin, et des habitants de Jérusalem.
Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
10 Et ils donnèrent cet argent à ceux qui faisaient les travaux, qu'on avait établis dans le temple du Seigneur; ils le donnèrent à ceux qui faisaient ce qu'il y avait à faire pour restaurer et raffermir le temple.
Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
11 Ils ordonnèrent aussi aux charpentiers et aux maçons d'acheter des pierres de taille et des solives pour recouvrir les logements que les rois de Juda avaient abattus.
Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
12 Et ces hommes se mirent fidèlement à l'œuvre, et ils furent surveillés par Jeth et Abdias, lévites de la maison de Mérari, par Zacharie et Mosollam, des fils de Caath, et par tous les lévites qui savaient chanter et jouer des instruments,
Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
13 Et les manœuvres et les ouvriers, chacun en son travail, étaient encore surveillés par les lévites scribes, juges et portiers.
sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
14 Or, tandis que l'on transportait l'argent donné pour le temple du Seigneur, Helcias, le prêtre, trouva un livre de la loi du Seigneur donnée par Moïse.
Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
15 Et Helcias prit la parole, et il dit à Saphan, le scribe: J'ai trouvé dans le temple du Seigneur un livre de la loi. Et Helcias donna le livre à Saphan.
Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
16 Et Saphan porta le livre au roi, et il lui rendit compte, disant: Voici le compte de tout l'argent qui a été remis à tes serviteurs chargés des travaux.
Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
17 Or, cet argent, trouvé dans le temple du Seigneur, avait été monnayé et distribué aux surveillants, puis aux ouvriers.
Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
18 Et Saphan en rendit compte au roi, et il ajouta: Helcias m'a donné un livre. Et Saphan le lut devant le roi.
Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
19 Et quand Josias ouït les paroles du livre de la loi, il déchira ses vêtements.
Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
20 Et il donna ses ordres à Helcias, à Achicam, fils de Saphan, à Abdom, fils de Michée, à Saphan, le scribe, à Asaïe, serviteur du roi, et il leur dit:
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
21 Allez et interrogez le Seigneur, pour moi et pour tout ce qui reste de Juda et d'Israël, au sujet des paroles du livre qui a été trouvé; car la colère du Seigneur s'est enflammée contre nous, parce que nos pères n'ont point obéi aux commandements du Seigneur, et n'ont point fait ce qui est écrit en ce livre.
Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
22 Or, Helcias et ceux à qui avait parlé le roi, allèrent trouver Olda, la prophétesse, femme de Sellem, file de Thécoé, fils d'Aras; elle observait les commandements, et demeurait à Jérusalem dans le second quartier, et ils lui parlèrent relativement à ces choses.
Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
23 Et elle leur répondit: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël; dites à l'homme qui vous a envoyés chez moi:
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
24 Voici ce que dit le Seigneur: Voilà que j'amène le mal sur ce lieu,' selon les paroles du livre qui a été lu devant le roi de Juda,
‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
25 En punition de ce qu'ils m'ont abandonné, de ce qu'ils ont brûlé de l'encens pour d'autres dieux, afin de m'irriter, par toutes les œuvres de leurs mains; car ma colère s'est enflammée contre ce lieu, et elle ne s'éteindra pas.
Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
26 Quant au roi de Juda qui vous a envoyés chez moi, pour interroger le Seigneur, dites-lui: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël: Aux paroles que tu as entendues,
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
27 Ton cœur a été rempli de crainte; tu t'es humilié devant moi, lorsque tu as ouï mes menaces contre ce lieu et contre ceux qui l'habitent; tu t'es humilié devant moi; tu as déchiré tes vêtements; tu as pleuré devant moi, et moi aussi j'ai entendu, dit le Seigneur.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
28 Voilà que je te réunis à tes pères; tu seras déposé en paix dans ton sépulcre, et tes yeux ne verront aucun des maux que j'amène sur ce lieu et sur ceux qui l'habitent. Et ils rapportèrent au roi ces paroles.
Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
29 Et le roi envoya des messagers, et il rassembla les anciens de Juda et de Jérusalem.
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
30 Et le roi monta au temple du Seigneur, avec tout Juda, tous les habitants de Jérusalem, les prêtres, les lévites et le peuple entier, depuis le petit jusqu'au grand, et il lut à leurs oreilles toutes les paroles du livre de l'alliance, trouvé dans le temple du Seigneur.
Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
31 Et le roi se tint debout sur le piédestal, et il fit une alliance devant le Seigneur, pour marcher devant le Seigneur, garder ses commandements, ses témoignages et ses ordonnances, de tout son cœur et de toute son âme, afin de se conformer à toutes les paroles de l'alliance écrites en ce livre.
Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
32 Et il fit lever tous ceux qui se trouvaient en Jérusalem; et Benjamin, et les habitants de Jérusalem firent une alliance dans le temple du Seigneur Dieu de leurs pères.
Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
33 Et Josias expulsa toutes les abominations de toute la terre des fils d'Israël, et il obligea tous ceux qui se trouvaient dans la ville et en Israël à servir, tous les jours de sa vie, le Seigneur leur Dieu; et il ne se détourna point du Seigneur Dieu de ses pères.
Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.

< 2 Chroniques 34 >