< 2 Chroniques 25 >
1 Amasias avait vingt-cinq ans lorsqu'il monta sur le trône, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem; sa mère s'appelait Joadan de Jérusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Et il fit ce qui est droit devant' Dieu, mais non avec plénitude de cœur.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 Lorsqu'il eut affermi sa royauté, il fit mettre à mort les serviteurs qui avaient tué le roi, son père.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 Mais il ne fit pas périr leurs fils, se conformant à l'alliance de la loi du Seigneur. Car il est écrit, et tel est le commandement de Dieu: Les pères ne mourront pas à cause de leurs enfants, et les fils ne mourront pas à cause de leurs pères; mais chacun portera la peine de son péché.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Ensuite, Amasias assembla la maison de Juda, et il les mit par familles paternelles sous des chefs de mille hommes et des centeniers, en Juda et en Jérusalem; il fit le dénombrement du peuple depuis vingt ans et au-dessus, et il trouva trois cent mille hommes capables de faire la guerre, sachant manier la javeline et le bouclier.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Il enrôla de plus cent mille hommes d'Israël, vaillants et robustes, au prix de cent talents d'argent.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 Mais un homme de Dieu vint le trouver, disant: Roi, n'emmène pas avec toi les troupes d'Israël, car le Seigneur n'est point avec Israël, ni avec aucun des fils d'Ephraïm.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Si tu les prends pour te renforcer, le Seigneur te mettra en fuite devant tes ennemis; car il appartient au Seigneur de renforcer une armée ou de la mettre en fuites.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Alors, Amasias dit à l'homme de Dieu: Que deviendront les cent talents d'argent que j'ai donnés aux troupes d'Israël? Et l'homme de Dieu répondit: Il ne tient qu'au Seigneur de t'en rendre beaucoup plus.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Et Amasias éloigna l'armée qui était venue près de lui d'Ephraïm, pour que chacun retournât en sa demeure. Et ils se courroucèrent vivement contre Juda, et ils s'en allèrent chez eux la colère dans l'âme.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Et Amasias se fortifia, et il prit son peuple, et il alla dans le val des Sels, et il tailla en pièces dix mille des fils de Seïr.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 Et les fils de Juda firent, en outre, dix mille prisonniers; ils les transportèrent sur la cime du précipice, et ils les jetèrent au bas des rochers, et ces hommes furent déchirés.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Et les hommes de l'armée qu'Amasias avait congédiés, pour qu'ils n'allassent pas en guerre avec lui, attaquèrent les villes de Juda, depuis Samarie jusqu'à Béthoron, et ils y tuèrent trois mille hommes, et ils y firent un riche butin.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Or, après qu'Amasias revint ayant vaincu l'Idumée, il en rapporta les dieux des fils de Séir, et il les tint pour des dieux véritables, et il se prosterna devant eux, et il leur fit des sacrifices.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Et la colère du Seigneur s'enflamma centre Amasias, et il lui envoya le prophète, qui lui dit: Pourquoi as-tu cherché les dieux d'un peuple qu'ils n'ont pu délivrer de tes mains?
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 Et, pendant que le prophète parlait encore, Amasias dit: Est-ce que je t'ai fait conseiller du roi? Contiens-toi, si tu ne veux être fustigé. Et le prophète garda le silence, et il se dit: Je sais que le Seigneur a résolu de te détruire, parce que tu as fais cette chose, et que tu refuses d'écouter mes conseils.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Ensuite, Amasias, roi de Juda, délibéra, et il envoya dire à Joas, fils de Joachaz, fils de Jéhu, roi d'Israël: Viens, que nous nous voyions face à face.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 Et Joas, roi d'Israël, envoya dire à Amasias: Le chardon du Liban envoya dire au cèdre du Liban: Donne en mariage ta fille à mon fils; mais voilà que les bêtes fauves des campagnes, qui sont dans le Liban, allaient venir, et les bêtes fauves vinrent, et elles foulèrent aux pieds le chardon.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Or, tu as dit: Voilà que j'ai vaincu l'Idumée. Et ton cœur impérieux s'est enorgueilli; reste donc en repos dans ta maison; car, pourquoi te mettre aux prises avec le malheur? Tu tomberas, et Juda avec toi.
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Mais Amasias ne l'écouta pas, car le Seigneur avait dessein de le livrer aux mains de Joas, parce qu'il avait cherché les dieux d'Edom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Joas, roi d'Israël, partit donc, et les deux rois se virent l'un l'autre à Bethsamys en Judée.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 Et Juda tourna le dos devant Israël, et chacun s'enfuit en sa demeure.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 Et Joas fit Amasias prisonnier, et il le ramena à Jérusalem; et il abattit un pan des remparts, long de quatre cents coudées, depuis la porte d'Ephraïm jusqu'à la porte de l'angle.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 Et il prit l'argent, l'or, tous les ornements qu'il trouva dans le temple du Seigneur, ce qui provenait d'Abdedom, les trésors du palais du roi, des otages, et il retourna dans Samarie.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 Amasias, fils de Joas, roi de Juda, vécut encore quinze ans après la mort de Joas, fils de Joachaz, roi d'Israël.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 Les restes des actes d'Amasias, les premiers et les derniers, ne sont-ils pas écrits au livre des Rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Dans le temps où Amasias s'était éloigné du Seigneur, un complot éclata contre lui, et il s'enfuit de Jérusalem à Lachis; mais les révoltés envoyèrent à sa poursuite, et, en cette ville, ils le tuèrent.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 Et ils l'enlevèrent sur un char, et ils l'ensevelirent auprès de ses pères dans la ville de David.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.