< 2 Chroniques 22 >
1 Et les habitants de Jérusalem proclamèrent roi à sa place Ochozias, son plus jeune fils, car l'armée de brigands qui était venue de l'Arabie et des bords de la mer, avait tué ses aînés; ainsi, Ochozias, fils de Joram, monta sur le trône de Juda.
Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Il avait alors vingt ans, et il régna un an à Jérusalem; le nom de sa mère était Athalie; elle était issue d'Ambri.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
3 Et il marcha dans les voies de la maison d'Achab, parce que sa mère par ses conseils l'entraînait à pécher.
Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
4 Et il fit le mal devant le Seigneur comme la maison d'Achab, car d'elle seule il prit conseil après la mort de son père, et il se perdit.
Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
5 Marchant donc selon ses conseils, il se joignit à Joram, fils d'Achab, roi d'Israël, pour livrer bataille, à Ramoth-Galaad, au roi de Syrie Azaël, quand des archers atteignirent Joram.
Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
6 Et Joram revint à Jezraël pour se guérir des blessures que les Syriens lui avaient faites en Ramoth-Galaad, lorsqu'il combattait Azaël, roi de Syrie. Et Ochozias, fils de Joram, roi de Juda, alla voir, en Jezraël, Joram, roi d'Israël, parce qu'il était malade.
saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
7 Et une catastrophe venant de Dieu arriva à Ochozias lorsqu'il y fut; car, alors Joram sortit avec lui contre Jéhu, fils de Namesseï, l'oint du Seigneur, suscité contre la maison d'Achab.
Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
8 Et au moment où Jéhu tirait vengeance de la maison d'Achab, il trouva là les princes de Juda, et les frères d'Ochozias employés à le servir, et il les tua.
Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
9 Ensuite, il ordonna de chercher Ochozias; on le prit en Samarie soignant ses blessures, on le conduisit à Jéhu qui le mit à mort, et on l'inhuma; car, dirent ces gens, il est issu de Josaphat qui de tout son cœur a cherché Dieu; il n'y avait plus personne de la maison d'Ochozias pour fortifier le pouvoir en son royaume.
Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
10 Et Athalie, mère d'Ochozias, voyant son fils mort, se leva et détruisit toute la race royale en Juda.
Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
11 Mais Josabeth, fille du roi Joram, enleva Joas, fils d'Ochozias; elle le déroba du milieu des fils du roi que l'on massacrait; et elle le mit, avec sa nourrice, dans une alcôve des chambres à coucher. Puis, Josabeth, fille de Joram, sœur d'Ochozias, femme de Joad le prêtre, le cacha d'Athalie, qui ne le tua pas.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
12 Il resta six ans avec Joad caché dans le temple de Dieu, pendant qu'Athalie régnait sur la terre.
Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.