< 2 Chroniques 16 >
1 Et, en la trente-huitième année du règne d'Asa, le roi d'Israël marcha contre Juda, et il bâtit Rhama pour empêcher le roi Asa de sortir et d'entrer.
A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
2 Et Asa prit tout l'argent et l'or des trésors, tant du temple que du palais, et il l'envoya au fils d'Ader, roi de Syrie, qui résidait à Damas, disant:
Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
3 Fais avec moi l'alliance qui existait entre ton père et le mien; voilà que je t'offre de l'argent et de l'or; viens, disperse Baasa, roi d'Israël, qu'il s'éloigne de mon royaume.
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
4 Et le fils d'Ader accueillit la demande d'Asa; il fit partir les chefs de ses armées contre les villes d'Israël, qui dévastèrent Ahion, Dan, Abelmaïn, et tout ce qui environne Nephthali.
Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
5 Quand Baasa l'apprit, il abandonna les constructions de Rhama, et il renonça à son entreprise.
Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
6 Et le roi Asa rentra en possession de tout Juda, et il prit à Rhama les pierres et les bois que Baasa avait employés pour la bâtir, et il s'en servit pour construire Gabaa et Maspha.
Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
7 En ce temps-là, Anani le prophète vint trouver Asa, roi de Juda, et il lui dit: Parce que tu t'es confié au roi de Syrie, et que tu n'as point eu foi en ton Dieu, l'armée de Syrie a échappé à tes mains.
A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
8 Les Ethiopiens et les Libyens n'avaient-ils pas une armée nombreuse, pleine d'audace, forte par ses cavaliers et sa multitude? Tu as eu foi en Dieu, et il te l'a livrée.
Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
9 Car les regards du Seigneur sont fixés sur la terre pour fortifier tout cœur parfait devant lui; en cela, tu as follement agi, et maintenant, tu seras toujours en guerre.
Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
10 Asa se mit en colère contre le prophète, et il le jeta en prison, tant il avait de courroux; et, en ce temps-là, Asa maltraita quelques-uns de son peuple.
Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
11 Et les actes d'Asa, les premiers et les derniers, sont écrits au livre des Rois de Juda et d'Israël.
Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
12 En la trente-neuvième année de son règne, Asa souffrit d'un mal aux pieds, dont il fut très-malade; et, en cette maladie, il ne chercha pas le Seigneur, mais les médecins.
A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
13 Et Asa s'endormit avec ses pères, et il mourut en la quarantième année de son règne.
Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
14 Et on l'ensevelit dans le sépulcre qu'il s'était creusé en la ville de David; or, on l'avait étendu sur sa couche, on l'avait rempli d'aromates et de toutes les substances dent se composent les parfums, et on lui fit de magnifiques funérailles.
Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.