< 2 Chroniques 13 >
1 En la dix-huitième année du règne de Jéroboam, Abias commença à régner sur Juda.
A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
2 Il régna trois ans à Jérusalem; et le nom de sa mère était Maacha, fille d'Uriel de Gabaon. Abias ne cessa pas d'être en guerre avec Jéroboam.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
3 Et il rangea en bataille une armée de quatre cent mille hommes vaillants, et Jéroboam lui en opposa huit cent mille, vaillants aussi.
Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
4 Alors Abias monta sur la colline de Salomon qui est dans les montagnes d'Ephraïm, et il dit: Jéroboam, écoute-moi ainsi que tout Israël.
Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
5 Ne devez-vous pas savoir que par une alliance sacrée, le Seigneur notre Dieu a donné pour toujours le royaume d'Israël à David et à ses fils.
Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
6 Mais, Jéroboam, fils de Nabat, serviteur de Salomon, fils de David, s'est levé et s'est révolté contre son maître.
Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
7 Et des hommes de pestilence, fils du péché, se sont joints à lui, qui s'est révolté contre Roboam, fils de Salomon, et Roboam, qui était jeune et d'un cœur craintif, n'osa lui tenir tête.
sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
8 Et vous maintenant, vous dites que vous résisterez au royaume du Seigneur que possèdent les fils de David; et vous êtes nombreux, et vous avez avec vous les veaux d'or qu'a faits Jéroboam, pour qu'ils soient vos dieux.
“Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
9 N'avez-vous pas chassé les prêtres du Seigneur, les fils d'Aaron et les lévites? Ne vous êtes-vous point fait des prêtres parmi le peuple de toute la terre? Quiconque arrive, pour se consacrer, avec un bœuf du troupeau et sept béliers, le voilà prêtre de ce qui n'est point dieu.
Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
10 Quant à nous, nous n'avons point abandonné le Seigneur; ce sont ses prêtres, fils d'Aaron, et ses lévites qui le servent, et qui journellement
“Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
11 Offrent des holocaustes au Seigneur, matin et soir, brûlent les parfums composés, déposent sur la table pure les pains de proposition, allument à la nuit le chandelier d'or et les lampes qui doivent brûler; car, nous observons les préceptes du Seigneur Dieu de nos pères, que vous avez abandonné.
Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
12 Voyez, le Seigneur et ses prêtres sont avec nous à notre tête; ce sont les trompettes sacrées qui nous donnent les signaux; fils d'Israël, gardez- vous de combattre le Seigneur, car vous ne réussirez à rien.
Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
13 Cependant, Jéroboam ramena sur les derrières de Juda une embuscade qu'il avait dressée; il fut ainsi lui-même devant Juda, et son embuscade derrière.
To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
14 Et Juda se retournant regarda, et voilà que la bataille était devant et derrière lui; alors, il cria au Seigneur, et les prêtres sonnèrent de la trompette.
Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
15 Et les hommes de Juda crièrent, et il advint, pendant qu'ils jetaient de grands cris, que le Seigneur frappa Jéroboam et Israël devant Abias et Juda.
mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
16 Et les fils d'Israël s'enfuirent devant Juda, et le Seigneur les livra au roi de Juda.
Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
17 Abias et son peuple les frappèrent d'une grande plaie, et cinq cent mille hommes vaillants succombèrent du côté d'Israël.
Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
18 Et, en ce jour-là, les fils d'Israël furent humiliés, et les fils de Juda prévalurent, parce qu'ils avaient espéré en Dieu.
Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
19 Abias poursuivit Jéroboam, il lui prit des villes: Béthel et ses bourgs, Mayne et ses bourgs, Ephron et ses bourgs.
Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
20 Et Jéroboam fut sans force sous le règne d'Abias; enfin, le Seigneur le frappa, et il mourut.
Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
21 Et Abias s'affermit, et il épousa quatorze femmes, dont il eut vingt-deux fils et seize filles.
Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
22 Le reste de l'histoire d'Abias, ses actions et ses discours, sont écrits au livre du prophète Addo.
Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.