< 1 Samuel 26 >

1 Après cela, des Ziphéens vinrent de la terre aride chez Saül à Gabaa, disant: Voilà que David est caché parmi nous sur la colline d'Echéla, en face de Jessème.
Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
2 Alors, Saül partit et descendit an désert de Ziph pour chercher David, avec trois mille hommes choisis en tout Israël.
Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
3 Il campa sur la route en la colline d'Echéla, vis-à-vis Jessème, tandis que David demeurait dans le désert. Et David vit que Saül était venu pour le poursuivre dans le désert.
Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
4 Et David envoya des éclaireurs, et il sut que Saül était arrivé en forces de Ceïla.
sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
5 Et David se leva sans bruit, et il se rendit au lieu où dormait Saül; il y avait là son général Abner, fils de Ner; Saül dormait sur un chariot couvert, ayant toute sa troupe campée autour de lui.
Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
6 David s'adressant à Abimélech le Hettéen, et à Abessa, fils de Sarvia, frère de Joab, leur dit: Qui viendra avec moi dans le camp jusqu'à Saül? Et Abessa répondit: Moi, je t'accompagnerai.
Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
7 Et David avec Abessa se glissa parmi la troupe pendant la nuit. Saül dormait d'un profond sommeil sur un chariot couvert, sa javeline plantée en terre près de sa tête; Abner et ses gens dormaient autour de lui.
Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
8 Abessa dit à David: Le Seigneur aujourd'hui enferme ton ennemi dans tes mains; je vais à l'instant, d'un seul coup de javeline, le faire rouler à terre; je n'aurai pas besoin de le frapper deux fois.
Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
9 Mais David dit à Abessa: Garde-toi de l'outrager; car qui peut sans crime porter la main sur l'oint du Seigneur?
Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
10 Et David ajouta: Vive le Seigneur! il ne mourra que quand le Seigneur le frappera, soit que son jour vienne et qu'il expire, soit qu'il succombe en combattant et aille rejoindre ses pères.
Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
11 Que le Seigneur me préserve de porter la main sur l'oint du Seigneur; maintenant, prends à son chevet sa javeline et la fiole d'eau, puis allons- nous-en.
Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
12 Ainsi, David prit auprès du chevet la javeline et la fiole d'eau, et ils s'en allèrent. Nul ne les vit, nul ne sut qu'ils étaient là, nul ne s'éveilla; tous dormaient, car le Seigneur avait fait tomber sur eux une profonde torpeur.
Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
13 David traversa le camp, et il s'arrêta au loin, du côté opposé, sur la cime de la montagne; il y avait entre eux et lui un grand espace.
Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
14 De là, David appela la troupe, et s'adressant à Abner, il dit: Ne répondras-tu point, Abner. Et Abner répondit, et il dit: Qui es-tu, toi qui appelles?
Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
15 Et David dit à Abner: N'es-tu pas un homme? Qui donc te vaut en Israël? Pourquoi ne gardes-tu pas le roi ton maître? Car quelqu'un du peuple est entré dans le camp pour le tuer.
Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
16 Ce n'est pas une bonne action que tu as faite là. Vive le Seigneur! vous êtes tous fils du meurtre, vous qui êtes commis à la garde du roi votre maître, l'oint du Seigneur. Maintenant, je te prie, la javeline du roi et la fiole d'eau qui étaient aussi auprès de son chevet, où sont-elles?
Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
17 Cependant, Saül reconnut la voix de David, et il dit: Est-ce ta voix, mon fils David? Et David répondit: C'est ton serviteur, Seigneur roi.
Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
18 Puis, il ajouta: Pourquoi le maître poursuit-il ainsi son serviteur? En quoi ai-je péché? Quelle iniquité a-t-on trouvée en moi?
Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
19 Maintenant donc que le roi mon maître écoute la parole de son serviteur. Si c'est Dieu qui t'excite contre moi, que ton sacrifice soit d'agréable odeur. Mais si ce sont des fils des hommes, maudits soient-ils devant le Seigneur, parce qu'ils m'ont chassé, de peur que je ne m'affermisse en l'héritage du Seigneur; et ils m'ont dit: Va-t'en, et sers d'autres dieux.
To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
20 Que mon sang ne soit point répandu sur la terre à la face du Seigneur, parce que le roi d'Israël est venu chercher ma vie, comme l'oiseau de nuit, quand il chasse dans les montagnes.
Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
21 Et Saül dit: J'ai péché, reviens, mon fils David, je ne te ferai point de mal, en récompense de ce qu'à tes yeux ma vie est précieuse. J'ai agi aujourd'hui comme un insensé, et j'ai ignoré beaucoup de choses.
Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
22 Et David reprit la parole; et il dit: Voilà la javeline du roi; que l'un des serviteurs approche, et qu'il la prenne.
Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
23 Et le Seigneur accordera à chacun, selon sa foi et son équité. Cette nuit, quand le Seigneur t'a livré à mes mains, je n'ai pas voulu porter la main sur l'oint du Seigneur;
Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
24 Et de même que ta vie a été précieuse à mes yeux, ma vie sera précieuse devant le Seigneur, et il m'abritera et il me délivrera de toutes mes afflictions.
Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
25 Et Saül dit à David: Béni sois-tu, mon fils, tu prospèreras, et tu seras très puissant. Alors, David s'en alla à sa demeure, et Saül retourna à la ville où il résidait.
Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.

< 1 Samuel 26 >