< 1 Samuel 14 >

1 Or, un jour vint où Jonathan, fils de Saül, dit au serviteur qui portait ses armes: Viens, allons à la station des Philistins du côté opposé au lieu où nous sommes; et il n'en dit rien à son père.
Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
2 Saül était campé au sommet de la colline, sous le grenadier qui est en Magdon, ayant avec lui environ six cents hommes.
Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
3 Et Achias, fils d'Achitob, frère de Jochabed, fils de Phinéès, fils d'Héli, était prêtre à Silo portant l'éphod. Et le peuple ne savait pas que Jonathan était parti.
A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
4 Au milieu du passage par où Jonathan voulait pénétrer parmi les Philistins, il y a un chemin bordé à droite et à gauche de rochers, qu'on appelle l'un Basès, l'autre Senna.
A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
5 Ce chemin était, d'une part, au nord de celui qui venait de Machmas; d'autre part, au midi de celui qui venait de Gabaa.
Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
6 Et Jonathan dit au serviteur qui portait ses armes: Viens, marchons à la station de ces incirconcis; voyons si le Seigneur fera quelque chose pour nous, car le Seigneur n'est pas astreint à sauver avec beaucoup d'hommes plutôt qu'avec un petit nombre.
Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
7 Le serviteur qui portait ses armes répondit: Fais selon le mouvement de ton cœur, je suis avec toi; mon cœur est comme ton cœur.
Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
8 Et Jonathan lui dit: Voici que nous allons monter au-dessus de ces hommes; puis nous roulerons en bas sur eux.
Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
9 S'ils nous disent: Halte-là; attendez que nous vous ayons parlé, nous nous arrêterons, et nous ne monterons pas pour les attaquer.
In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
10 Mais, s'ils nous disent: Montez vers nous, nous monterons, car le Seigneur nous les a livrés, ce sera là notre signe.
Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
11 Et tous les deux parvinrent à la station des Philistins, qui se dirent: Voici des Hébreux; ils sortent des cavernes où ils étaient cachés.
Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
12 Aussitôt, les hommes de la station s'adressèrent à Jonathan et à celui qui portait ses armes, disant: Montez vers nous, et nous vous ferons connaître quelque chose. A ces mots, Jonathan dit à celui qui portait ses armes: Suis- moi, le Seigneur nous les a livrés.
Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
13 Jonathas monta donc en s'aidant des mains comme des pieds, et celui qui portait ses armes le suivit; les Philistins se trouvèrent face à face avec Jonathas quand celui-ci se mit à les frapper; son serviteur alors arrivait derrière lui.
Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
14 Or, ce fut le premier fait d'armes de Jonathan et de son serviteur; ils leur tuèrent une vingtaine d'hommes, avec des dards, des frondes et des cailloux.
A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
15 Et l'effroi se répandit dans le camp et la plaine; toutes les troupes de la station et les pillards au dehors, saisis de stupeur, furent incapables d'agir; la contrée trembla, et le Seigneur répandit partout l'épouvante.
Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
16 Cependant, les éclaireurs de Saül virent de Gabaa le trouble du camp et les hommes qui fuyaient çà et là.
Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
17 Et Saül dit aux siens: Examinez bien, et voyez qui des nôtres est parti; ils cherchèrent, et l'on ne trouva ni Jonathan ni celui qui portait ses armes.
Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
18 Et Saül dit à Achias: Présente l'éphod; car, en ce jour-là, Achias portait l'éphod devant Israël.
Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
19 Pendant que Saül parlait au prêtre, la rumeur du camp des Philistins, toujours croissante, se répandit et se répandit. Et Saül dit au prêtre: Joins les mains.
Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
20 Saül aussitôt, avec toute sa troupe, se porta au combat; il vit les ennemis tournant les uns contre les autres leurs épées; c'était une confusion vraiment très grande.
Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
21 Les Hébreux, devenus depuis peu esclaves dans le camp des Philistins, se soulevèrent pour se joindre à Israël, à Saül, à Jonathan.
Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
22 Et tous ceux d'Israël, qui s'étaient cachés dans les montagnes d'Ephraïm, apprirent que les Philistins fuyaient; et ils se mirent à leur poursuite;
Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
23 Et, ce jour-là, le Seigneur sauva Israël. La bataille fut livrée en Barnoth, et Saül eut environ dix mille hommes avec lui. On combattit dans toutes les villes des montagnes d'Ephrem.
Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
24 Or, Saül, ce jour-là, commit un grand péché par ignorance: il prononça une malédiction contre le peuple, disant: Maudit soit l'homme qui mangera avant le soir; car je veux avant tout tirer vengeance de mon ennemi. Et nul, parmi le peuple, ne goûta de pain, tandis que, sur toute la terre, chacun prenait son repas.
A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
25 Et devant le champ de bataille, la forêt de Jaal était remplie de miel.
Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
26 Le peuple passait près des abeilles, et s'en allait devisant, et nul n'osait porter la main à sa bouche; car ils redoutaient l'imprécation portée au nom du Seigneur.
Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
27 Jonathan, qui n'avait point entendu son père adjurer le peuple, étendit la pointe de la baguette qu'il tenait à la main, la trempa dans un rayon de miel, porta la main à sa bouche, et ses yeux recouvrèrent la vue.
Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
28 Aussitôt, l'un du peuple s'écria, et lui dit: Ton père a vivement adjuré le peuple; il a dit: Maudit soit l'homme qui mangera avant le soir. Or, le peuple était à bout de forces.
Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
29 Jonathan le savait, et il dit: Mon père trouble la terre promise; sois témoin que mes yeux ont recouvré la vue, dès que j'ai eu goûté un peu de ce miel.
Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
30 Si le peuple s'était rassasié des vivres qu'il a trouvé parmi les dépouilles des ennemis, il y eût eu de ceux-ci un plus grand carnage.
Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
31 Or, ce jour-là, il avait exterminé nombre de Philistins à Machmas, et le peuple était accablé de fatigue.
A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
32 Et, le soir venu, le peuple, se jetant sur les dépouilles, prit des brebis, des bœufs, des veaux, et les égorgea à terre; puis, il les mangea avec leur sang.
Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
33 Et des gens le rapportèrent à Saül, disant: Le peuple a péché contre le Seigneur, il a mangé des chairs avec du sang. Et Saül dit: Roulez-moi de Getthaim ici une grande pierre.
Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
34 Cela fait, Saül dit à ces gens: Dispersez-vous parmi le peuple, dites- leur d'amener ici chacun son veau ou sa brebis; qu'on égorge les victimes sur cette pierre, et vous, gardez-vous de pécher envers le Seigneur en les mangeant avec leur sang. Le peuple amena donc là ce qu'il avait à conduire, et on égorgea les victimes au même lieu.
Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
35 Et Saül y bâtit un autel au Seigneur; ce fut le premier autel que Saül éleva au Seigneur.
Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
36 Ensuite, Saül dit: Poursuivons toute la nuit les Philistins, nous leur ferons des prisonniers, jusqu'à ce que le jour paraisse, et nous n'en laisserons pas échapper un seul. A quoi ils répondirent: Fais ce que bon te semble. Mais le prêtre dit: Allons d'abord au Seigneur.
Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
37 Et Saül fit cette question au Seigneur: Si je poursuis les Philistins, les livrerez-vous aux mains d'Israël? Le Seigneur ne lui répondit point.
Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
38 Et Saül dit: Faites venir ici tous les rangs d'Israël: que l'on sache lequel d'entre eux aujourd'hui a péché.
Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
39 Car, vive le Seigneur qui a sauvé Israël, s'il est reconnu que c'est Jonathan mon fils, Jonathan sera mis à mort. Et, parmi le peuple, nul ne répondit.
Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
40 Alors, Saül dit à chaque homme d'Israël: Vous serez asservis; moi et mon fils Jonathan nous serons asservis. Et le peuple dit à Saül: Fais ce que bon te semble
Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
41 Et Saül dit: Seigneur Dieu d'Israël, pourquoi refusez-vous aujourd'hui de répondre à votre serviteur? Est-il en moi ou en mon fils Jonathan quelque iniquité? Donnez-nous des signes, et, s'ils nous accusent, donnez à votre peuple Israël, donnez-lui le privilège de l'innocence. Et le sort désigna Saül et Jonathan; le peuple sortit innocent.
Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
42 Puis, Saül dit: Agitez les sorts entre moi et Jonathan mon fils. Celui qu'indiquera le Seigneur, qu'il soit mis à mort. Le peuple, à ces mots, dit à Saül: Cela ne peut être; mais Saül imposa silence au peuple. L'on agita donc les sorts entre lui et Jonathan son fils, et le sort désigna Jonathan.
Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
43 Alors, Saül dit à Jonathan: Déclare-moi ce que tu as fait. Jonathan le lui avoua, et dit: J'ai goûté, au bout de la baguette que je tenais à la main, un peu de miel, et voilà que je meurs.
Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
44 Et Saül dit: Que le Seigneur me punisse, et qu'il me punisse encore, si tu ne meurs aujourd'hui.
Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
45 Mais le peuple dit à Saül: Celui qui vient de sauver si bravement Israël mourra-t-il? Vive le Seigneur! pas un cheveu ne tombera de sa tête, car le peuple de Dieu a été vainqueur aujourd'hui. Le peuple, en ce jour-là, pria donc pour Jonathan, et il ne mourut pas.
Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
46 Et Saül renonça à poursuivre les Philistins; et ceux-ci retournèrent en leur pays.
Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
47 Saül, en obtenant par le sort la royauté, avait été chargé par le sort de faire œuvre pour Israël; tout alentour, il combattit donc ses ennemis: Moab, les fils d'Ammon, les fils d'Edom, Béthéor, le roi de Suba et tous les Philistins.
Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
48 Il fut un homme fort; il vainquit Amalec, et il tira Israël des mains de ceux qui le foulaient aux pieds.
Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
49 Les fils de Saül étaient Jonathan, Jessui et Melchisa; ses filles se nommaient: la première, Mérob, la plus jeune, Michol.
’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
50 Le nom de sa femme était Achinoom, fille d'Achimaas; son général s'appelait Abner, fils de Ner, parent de Saül.
Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
51 Car Cis était père de Saül, et Ner, père d'Abner, était fils de Jamin, fils d'Abiel.
Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
52 La guerre contre les Philistins fut rude pendant toute la vie de Saül, et tous les hommes puissants et les braves que voyait Saül, il les réunissait autour de lui.
Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.

< 1 Samuel 14 >