< 1 Samuel 12 >

1 Ensuite, Samuel dit à tout Israël: Voyez, j'ai fait tout ce que vous m'avez demandé, et je vous ai donné un roi.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 Voici maintenant qu'un roi marche à votre tête; pour moi, je suis vieux et vais me tenir en repos; je laisse parmi vous mes fils, après avoir marché à votre tête depuis ma naissance jusqu'à ce jour.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 Or, répondez-moi devant le Seigneur et devant son oint: A qui de vous ai- je pris un bœuf ou un âne? Qui de vous ai-je opprimé? qui ai-je violenté? de qui ai-je accepté l'offrande de quoi que ce soit, même d'une chaussure? Déclarez-le, et je restituerai.
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 Et chacun dit à Samuel: Tu n'as point commis d'iniquités envers nous; tu ne nous as point opprimés, tu ne nous a point violentés, tu n'as rien pris à aucun d'entre nous.
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 Et Samuel dit au peuple: Le Seigneur est témoin, l'oint du Seigneur est témoin aujourd'hui que vous n'avez rien à me réclamer; et ils dirent: Témoin.
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Samuel dit encore au peuple: Je prends à témoin le Seigneur qui a suscité Moïse et Aaron, qui a tiré vos pères de l'Égypte.
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Maintenant, tenez-vous tranquilles; je vais vous juger devant le Seigneur, je vous dévoilerai toute la justice du Seigneur, tout ce qu'il a fait pour vous et pour vos pères.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 Lorsque Jacob et ses fils se furent établis en Égypte, l'Égypte les humilia; et vos pères crièrent au Seigneur, et le Seigneur envoya Moïse avec Aaron qui conduisirent vos pères hors de l'Égypte, et les mirent en possession de cette terre promise.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 Ensuite, vos pères méconnurent le Seigneur leur Dieu, et il les livra aux mains de Sisara, général de Jabin, roi d'Azor; puis, aux mains des Philistins; puis, aux mains du roi de Moab, et il combattit du côté de leurs ennemis.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 Alors, ils crièrent au Seigneur; ils dirent: Nous avons péché, car nous avons abandonné le Seigneur, et nous avons servi Baal dans les bois sacrés; délivrez-nous des mains de nos ennemis, et nous vous servirons.
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 Et le Seigneur a suscité Jérobaal, puis Barac, puis Jephté, puis Samuel; il vous a délivrés des mains des ennemis qui vous entourent, et vous avez habité en paix vos maisons.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 Et, vous avez vu récemment que Naas, roi des fils d'Ammon, marchait contre vous, et vous avez dit: Nous le voulons, il faut qu'un roi règne sur nous. Et cependant, le Seigneur notre Dieu était notre roi!
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 Or maintenant, voici le roi que vous avez élu; vous voyez que le Seigneur vous a donné un roi, et vous prospèrerez,
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 Si vous craignez le Seigneur, si vous le servez, si vous êtes dociles à sa voix, si vous ne résistez point à ses paroles, si vous et votre roi vous marchez avec le Seigneur.
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 Mais si vous êtes indociles à la voix du Seigneur, si vous résistez à ses paroles, la main du Seigneur s'appesantira sur vous et sur votre roi.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 Maintenant retirez-vous tranquilles, et vous verrez le grand prodige que le Seigneur va faire éclater à vos yeux.
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 N'est-ce pas aujourd'hui la moisson du froment? Je vais invoquer le Seigneur; il vous enverra le tonnerre et la pluie, et vous reconnaîtrez et vous verrez combien a été grande votre méchanceté devant le Seigneur, quand vous avez demandé pour vous un roi.
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Samuel invoqua donc le Seigneur, et, en ce jour-là, le Seigneur envoya le tonnerre et la pluie. Alors, tout le peuple eut une grande crainte du Seigneur et de Samuel.
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 Et tout le peuple dit à Samuel: Prie le Seigneur ton Dieu pour tes serviteurs, afin que nous ne mourions pas, parce qu'à nos péchés nous avons ajouté la faute de demander pour nous un roi.
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 Et Samuel dit au peuple: N'ayez point de crainte; vous avez commis réellement tous cette faute; mais ne vous écartez pas des voies du Seigneur, servez-le de tout votre cœur;
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 Ne vous laissez pas égarer par des dieux qui n'existent point, qui ne peuvent rien, qui ne délivrent personne, puisqu'ils ne sont que néant.
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 Tandis que le Seigneur, à cause de son grand nom, ne répudiera pas son peuple, car le Seigneur vous a visiblement choisis pour être son peuple.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 Pour moi, je me garderai de pécher contre le Seigneur, et de cesser de prier pour vous. Je servirai le Seigneur, et je vous montrerai la voie bonne et droite.
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 Mais craignez le Seigneur, servez-le dans la vérité et de tout votre cœur, puisque vous avez vu les grandes choses qu'il a faites parmi vous.
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 Et si vous retombez dans le péché, vous périrez vous et votre roi.
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.

< 1 Samuel 12 >