< 1 Rois 18 >
1 Après bien des jours, la parole du Seigneur vint à Elie pendant la troisième année, disant: Pars, présente-toi devant Achab, et je donnerai de la pluie à la terre.
Bayan dogon lokaci, a cikin shekara ta uku, maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce, “Tafi, ka gabatar da kanka ga Ahab, zan kuwa aika da ruwan sama a ƙasar.”
2 Et Elie partit pour se présenter devant Achab. En ce temps-là, il y avait à Samarie une famine très grande.
Saboda haka Iliya ya tafi ya gabatar da kansa ga Ahab. Yanzu dai yunwa ta tsananta a Samariya,
3 Et Achab appela son économe Abdias; or, Abdias craignait beaucoup le Seigneur.
Ahab kuma ya aika a kawo Obadiya, sarkin fadansa (Obadiya dai cikakken mai gaskata da Ubangiji ne.
4 Quand Jézabel frappait les prophètes du Seigneur, Abdias avait pris cent hommes qui prophétisaient; il les avait cachés cinquante par cinquante dans des cavernes où il les avait nourris de pain et d'eau.
Yayinda Yezebel tana kisan annabawan Ubangiji, Obadiya ya ɗauki annabawa ɗari ya ɓoye a kogwanni biyu, hamsin a kowanne, ya kuma tanada musu abinci da kuma ruwa.)
5 Et Achab dit à Abdias: Viens, parcourons la contrée, visitons les torrents et les fontaines; peut-être trouverons-nous de l'herbe; nous y ferons paître les chevaux et les mules, et ils ne périront pas dans les étables.
Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka ratsa ƙasar zuwa dukan maɓulɓulai da fadamu. Mai yiwuwa ka sami ciyawa mu ba dawakai da alfadarai don su rayu, don kada mu kashe dabbobinmu.”
6 Et ils se partagèrent les territoires à visiter; Achab prit une route; Abdias, de son côté, en prit une autre.
Saboda haka suka raba ƙasar da za su ratsa, Ahab zai tafi gefe ɗaya, Obadiya kuma yă bi gefe ɗaya.
7 Comme Abdias s'en allait seul sur un chemin, Elie arriva seul à sa rencontre. Abdias, pressant le pas, tomba la face contre terre, et il dit: Est-ce bien toi, Elie, mon maître?
Yayinda Obadiya yana tafiya, sai Iliya ya sadu da shi. Obadiya ya gane shi, ya rusuna har ƙasa, ya ce, “Kai ne, shugabana, Iliya?”
8 Elie répondit: C'est moi; pars, et dis à ton maître: Voici Elie.
Iliya ya amsa, ya ce, “I, je ka faɗa wa maigidanka cewa, ‘Iliya yana a nan.’”
9 Abdias reprit: Quel péché ai-je fait pour que tu livres ton serviteur aux mains d'Achab, afin qu'il me fasse mourir.
Obadiya ya yi tambaya, “Me na yi da ba daidai ba, da kake miƙa bawanka ga Ahab don yă kashe?
10 Vive le Seigneur ton Dieu! il n'est ni peuple ni royaume où mon maître n'ait envoyé pour te prendre, et quand on disait: Elie n'est pas ici, il portait la flamme en ce royaume et en ses campagnes, parce qu'il ne t'avait point trouvé.
Na rantse da Ubangiji Allahnka, babu al’umma ko masarauta da mai girma sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka can, sai yă sa mulkin ko al’ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba.
11 Et maintenant, tu veux que je parte et que je dise à ton maître: Voici Elie!
Amma yanzu kana faɗa mini in tafi wurin mai girma in ce, ‘Iliya yana a nan.’
12 Voici ce qui adviendra: Lorsque je me serai éloigné de toi, l'Esprit du Seigneur te ravira en une terre je ne sais laquelle; et je me présenterai devant Achab et je t'annoncerai; mais lui, ne te trouvant pas, me fera mourir; or, ton serviteur, depuis son enfance, a la crainte de Dieu.
Ban san inda Ruhun Ubangiji zai kai ka sa’ad da na bar ka ba. In na tafi na faɗa wa Ahab bai kuma same ka a nan ba, zai sa a kashe ni. Tuna fa, ni bawanka, na yi wa Ubangiji sujada tun ina saurayi.
13 Ne sais-tu pas, ô mon maître, que quand Jézabel tuait les prophètes du Seigneur, j'ai caché cent prophètes du Seigneur, cinquante par cinquante, en des cavernes, et que je les ai nourris de pain et d'eau?
Ranka yă daɗe, ashe, ba a faɗa maka abin da na yi lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji ba? Yadda na ɓoye annabawa ɗari, na sa su hamsin-hamsin a kogwanni biyu, na yi ta ba su abinci da ruwa.
14 Et maintenant, tu veux que je parte et que je dise à mon maître: Voici Elie! Mais il me tuera.
Yanzu fa, kana ce in tafi wurin mai girma sarki, in ce, ‘Iliya yana a nan.’ Ai, zai kashe ni!”
15 Elie reprit: Vive le Seigneur Dieu des armées, devant qui je suis! aujourd'hui même Achab me verra.
Iliya ya ce, “Na rantse da Ubangiji Maɗaukaki, wanda nake bauta wa, tabbatacce zan gabatar da kaina ga Ahab a yau.”
16 Abdias alla donc à la rencontre d'Achab; il lui annonça le prophète, et Achab accourut au-devant d'Elie.
Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya.
17 Aussitôt qu'il aperçut Elie, il s'écria: Es-tu donc celui qui pervertit Israël?
Sa’ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne wannan, kai mai tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila?”
18 Et le prophète répondit: Ce n'est point moi qui pervertis Israël, mais toi-même et la maison de ton père; car, vous abandonnez le Seigneur votre Dieu pour suivre Baal.
Iliya ya amsa, ya ce, “Ban tā-da-na-zaune-tsaye a Isra’ila ba. Amma kai da iyalin mahaifinka, ku kuka tā-da-na-zaune-tsaye. Ka ƙyale umarnai Ubangiji, ka bi Ba’al.
19 Donne à ce moment tes ordres: rassemble devant moi, sur le mont Carmel, tout le peuple des dix tribus avec les quatre cent cinquante prophètes de l'opprobre, et les quatre cents prophètes des bois sacrés, qui mangent à la table de Jézabel.
Yanzu ka tara mutane daga dukan Isra’ila su sadu da ni a kan Dutsen Karmel. Ka kuma kawo annabawa ɗari huɗu da hamsin na Ba’al, da kuma annabawa ɗari huɗu na Ashera, waɗanda suke ci a teburin Yezebel.”
20 Et Achab envoya par tout Israël; et il rassembla sur le mont Carmel tous les prophètes.
Sai Ahab ya aika a duk fāɗin Isra’ila, ya kuma tattara annabawan a kan Dutsen Karmel.
21 Devant eux tous, il mena Elie, et celui-ci leur dit: Jusqu'à quand boiterez-vous des deux jambes? Si le Seigneur est Dieu, suivez le Seigneur; si Baal est Dieu, suivez Baal. Et le peuple ne souffla mot.
Iliya ya je gaban mutane ya ce, “Har yaushe za ku yi ta yawo tsakanin ra’ayoyi biyu? In Ubangiji ne Allah, ku bi shi; amma in Ba’al Allah ne, ku bi shi.” Mutane dai ba su ce uffam ba.
22 Elie dit ensuite au peuple: Il n'y a plus que moi de prophète du Seigneur; les prophètes de Baal sont quatre cent cinquante, et les prophètes des bois sacrés quatre cents.
Sai Iliya ya ce musu, “Ni ne kaɗai annabin Ubangiji da ya rage, amma Ba’al yana da annabawa ɗari huɗu da hamsin.
23 Que l'on nous donne deux bœufs; qu'ils en choisissent un pour eux, qu'ils le séparent par membres, qu'ils le posent sur le bûcher sans qu'on y mette le feu; moi cependant j'apprêterai de même l'autre bœuf, et je n'allumerai point le bûcher.
Ku samo mana bijimai biyu. Bari su zaɓa ɗaya wa kansu, bari kuma su yanka shi kucu-kucu su sa a itace, sai dai, kada su sa wuta a kansa. Ni kuwa zan shirya ɗaya bijimin in sa a kan itace, ni ma, ba zan sa wuta a kansa ba.
24 Criez alors au nom de vos dieux, et moi j'invoquerai le nom du Seigneur mon Dieu; le Dieu qui nous exaucera en envoyant de la flamme, celui-là est Dieu. A ces mots tout le peuple répondit, et il dit: Tu as bien parlé.
Sa’an nan ku kira bisa sunan allahnku, ni kuwa zan kira bisa sunan Ubangiji. Duk allahn da ya amsa ta wurin wuta, shi ne Allah.” Sai dukan jama’a suka ce, “Abin nan da faɗa yana da kyau.”
25 Aussitôt, Elie dit aux prophètes de l'opprobre: Choisissez pour vous l'un des bœufs, et apprêtez-le les premiers, car vous êtes nombreux; invoquez le nom de vos dieux, et n'allumez pas le bûcher.
Iliya ya ce wa annabawan Ba’al, “Ku ku fara zaɓi bijimi ɗaya, ku shirya, da yake kuna da yawa. Ku kira a bisa sunan allahnku, amma kada ku ƙuna wuta.”
26 Ils prirent le bœuf, ils l'apprêtèrent, ils invoquèrent le nom de Baal depuis l'aurore jusqu'au milieu du jour, et ils dirent: Exaucez-nous, ô Baal, exaucez-nous. Mais il n'y avait point de voix pour leur répondre, point d'oreilles pour les ouïr, et ils passaient et repassaient devant l'autel qu'ils avaient élevé.
Sai suka ɗauki bijimin da aka ba su suka shirya shi. Sa’an nan suka kira bisa sunan Ba’al daga safe har tsakar rana. Suna ihu, “Ya Ba’al, ka amsa mana!” Amma babu wata amsa, babu wani da ya amsa. Suka yi ta rawa kewaye da bagaden da suka yi.
27 Le milieu du jour vint, et le Thesbite Elie les railla, et il dit; Invoquez-le à grands cris, puisque vous le dites dieu; il est peut-être à méditer, il est peut-être en affaire, ou peut-être il dort, et il se réveillera.
Da tsakar rana, Iliya ya fara yin musu ba’a. Ya ce, “Ku yi ihu da ƙarfi, tabbatacce shi allah ne! Mai yiwuwa yana cikin zurfin tunani, ko dai aiki ya yi masa yawa, ko ya yi tafiya. Mai yiwuwa yana barci ne, dole a tashe shi.”
28 Ils firent donc leurs invocations à grands cris; puis, selon leurs rites, ils se firent des entailles avec des poignards et des lancettes, de telle sorte que le sang ruissela sur eux.
Sai suka yi ta ihu da ƙarfi suna tsattsaga kansu da takuba da māsu, yadda al’adarsu take, sai da jininsu ya yi ta zuba.
29 Et ils prophétisèrent jusqu'à ce que le soleil commençât à décliner. Le moment étant venu où l'on place sur l'autel les victimes, Elie le Thesbite dit aux prophètes des abominations: Retirez-vous maintenant, et je ferai mon holocauste. Et ils se retirèrent, et ils partirent.
Tsakar rana ta wuce, suka ci gaba da ƙoƙari, suna annabci har lokacin miƙa hadayar yamma ya yi. Amma babu wani da ya tanƙa, babu wani da ya amsa, babu wanda ya kula.
30 Alors, Elie dit au peuple: Approchez-vote de moi, et tout le peuple s'approcha de lui.
Sa’an nan Iliya ya ce wa dukan mutane, “Ku zo nan wurina.” Suka zo wurinsa, ya kuma shirya bagaden Ubangiji, da ya riga ya zama kufai.
31 Et Elie prit douze pierres selon le nombre des tribus issues d'Israël à qui le Seigneur avait dit: Israël sera ton nom.
Iliya ya ɗauki duwatsu goma sha biyu, ɗaya don kowace kabila zuriyar Yaƙub, wanda maganar Ubangiji ta zo masa, cewa, “Sunanka zai zama Isra’ila.”
32 Et il mit en œuvre ces pierres au nom du Seigneur, et il répara l'autel qui avait été renversé; autour de l'autel il creusa une rigole, qui eût contenu deux mesures de semence.
Da waɗannan duwatsun ya gina bagade cikin sunan Ubangiji, ya kuma haƙa wuriya kewaye da shi, isashe da zai ci garwa biyu na irin ƙwayar gyada.
33 Et il empila du bois fendu sur l'autel qu'il avait construit, sépara par membres l'holocauste, le posa sur les éclats de bois, et l'empila sur l'autel.
Ya shirya itace, ya yayyanka bijimin kucu-kucu, ya shimfiɗa shi a itacen. Sa’an nan ya ce musu, “Ku cika manyan tuluna da ruwa, ku zuba a kan hadayar da kuma a kan itacen.” Suka zuba.
34 Puis, il dit: Prenez-moi quatre cruches d'eau que vous répandrez sur l'holocauste et sur le bois. Ainsi firent-ils, et il dit: Redoublez; ils redoublèrent, et il dit: Recommencez une troisième fois, et ils recommencèrent.
Ya ce, “Ku sāke yin haka,” sai suka sāke yin haka. Ya umarta, “Ku yi haka sau na uku,” suka kuma yi haka sau na uku.
35 Et l'eau coula autour de l'autel, et la rigole en fut remplie.
Ruwan ya gangara kewaye da bagaden har ma ya cika wuriyar.
36 Et Elie cria au ciel, disant: Seigneur Dieu d'Abraham, d'Isaac et d'Israël, exaucez-moi, Seigneur, exaucez-moi aujourd'hui en m'envoyant de la flamme; que tout le peuple reconnaisse que vous êtes le Seigneur Dieu d'Israël, que je suis votre serviteur, et que je n'ai rien fait, sinon par vous.
A lokacin hadaya, sai annabi Iliya ya zo gaba ya yi addu’a, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Ibrahim, na Isra’ila da kuma na Yaƙub, bari a sani a yau cewa kai Allah ne a cikin Isra’ila, a kuma san cewa ni bawanka ne, na kuma yi dukan waɗannan abubuwa bisa umarninka.
37 Exaucez-moi, Seigneur, exaucez-moi; que le peuple reconnaisse que vous êtes le Seigneur Dieu, et vous convertirez le cœur de ce peuple.
Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, saboda waɗannan mutane su san cewa kai, ya Ubangiji, kai ne Allah, su kuma san cewa kana sāke juye zukatansu zuwa gare ka.”
38 Et une flamme descendit tu ciel, envoyée par le Seigneur; elle dévora l'holocauste, le bûcher, l'eau de la rigole; elle effleura les pierres de l'autel et la terre.
Sai wutar Ubangiji ya fāɗo, ya cinye hadayar, itacen, duwatsun da kuma ƙasar, ya lashe ruwan da yake cikin wuriyar.
39 Et le peuple tomba la face contre terre, et il dit: En vérité, le Seigneur Dieu est le seul Dieu.
Sa’ad da mutane suka ga wannan, sai suka rusuna, suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji, shi ne Allah! Ubangiji, shi ne Allah!”
40 Elie dit ensuite au peuple: Saisissez les prophètes de Baal, que pas un seul ne soit épargné. Ils les saisirent, et Elie les traîna au torrent de Cisson, et là, il les égorgea.
Sa’an nan Iliya ya umarce su, ya ce, “Ku kama annabawan Ba’al, kada ku bar waninsu yă tsere!” Suka kama su, Iliya kuwa ya sa aka gangara da su zuwa Kwarin Kishon, aka yayyanka su a can.
41 Elie dit ensuite à Achab: Pars, mange et bois; car il y a un bruit de pluie qui arrive.
Sai Iliya ya ce wa Ahab, “Ka haura gida, ka ci, ka sha, gama ina jin motsin ruwan sama mai yawa.”
42 Et Achab partit pour manger et boire; et le prophète monta sur le Carmel; là, il se pencha vers la terre, la tête entre les genoux.
Sai Ahab ya ruga don yă ci, yă sha, amma Iliya ya hau kan ƙwanƙolin Karmel, ya rusuna ƙasa, ya sa fuska a tsakanin gwiwarsa.
43 Puis, il dit à son serviteur: Va, et regarde du côté de la mer. Le serviteur regarda, et il dit: il n'y a rien. Mais son maître lui dit: Retournes-y sept fois.
Ya ce wa bawansa, “Tafi ka dubi wajen teku.” Sai bawan ya haura ya duba. Ya ce, “Ba kome a can.” Sau bakwai Iliya ya ce, “Koma.”
44 Et le serviteur y retourna sept fois; à la septième fois il vit un petit nuage semblable au pied d'un homme, et ce nuage amenait de l'eau; le maître alors dit au serviteur: Va trouver Achab, et dis-lui: Attelle ton char et mets-toi en route, de peur que la pluie ne te surprenne.
Sau na bakwai, bawan ya ce, “Wani girgije ƙarami kamar hannun mutum yana tasowa daga teku.” Sai Iliya ya ce, “Je ka faɗa wa Ahab, ‘Shirya keken yaƙinka, ka gangara kafin ruwan sama yă tare ka.’”
45 Bientôt çà et là le ciel s'obscurcit de nuées, le vent souffla, et il tomba une grande pluie. Et Achab, en pleurant, s'en alla à Jezraël.
Ana cikin haka, sarari ya ƙara duhunta da girgije, iska ta taso, sai ruwan sama kamar da bakin kwarya ya sauko, Ahab kuwa ya hau zuwa Yezireyel.
46 Et la main du Seigneur s'étendit sur Elie, et il serra sur ses reins sa ceinture, et il courut devant Achab jusqu'à Jezraël.
Ikon Ubangiji ya sauko a kan Iliya, ya sha ɗamara, ya ruga a guje a gaban Ahab har zuwa Yezireyel.