< 1 Rois 16 >

1 Et la parole du Seigneur vint à Jéhu, fils d'Anani; celui-ci dit à Baasa:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Yehu ɗan Hanani game da Ba’asha,
2 En punition de ce qu'après avoir été, par moi, tiré de la poussière et élevé sur le trône d'Israël, tu as marché dans la voie de Jéroboam, tu as fait tomber dans le péché tout mon peuple d'Israël, qui, par ses vanités, a excité ma colère,
“Na ɗaga ka daga ƙura na mai da kai shugaban mutanena Isra’ila, amma ka yi tafiya a hanyoyin Yerobowam, ka kuma sa mutanena Isra’ila suka yi zunubi, ka tsokane ni na yi fushi ta wurin zunubansu.
3 Je susciterai des ennemis contre toi Baasa et contre toute ta maison, et je leur livrerai ta maison comme je t'ai livré la maison de Jéroboam, fils de Nabat.
Saboda haka ina gab da cinye Ba’asha da gidansa, zan kuma mai da gidanka kamar na Yerobowam ɗan Nebat.
4 Les chiens dévoreront celui du sang de Baasa qui mourra dans la ville; et les oiseaux du ciel dévoreront celui qui mourra dans les champs.
Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ba’asha da suka mutu a birni, tsuntsaye kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
5 Quant au reste de l'histoire de Baasa, n'est-il pas écrit au livre des Faits et gestes des rois d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Ba’asha, abin da ya yi, da kuma nasarorinsa, an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
6 Et Baasa s'endormit avec ses pères; il fut enseveli à Thersa, et son fils régna à sa place.
Ba’asha ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Tirza. Sai Ela ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
7 Or, le Seigneur avait parlé par la voix de Jéhu, fils d'Anani, contre Baasa et sa maison, à cause de tout le mal qu'il avait fait devant le Seigneur, pour irriter le Seigneur par les œuvres de ses mains, et pour que sa maison devînt comme celle de Jéroboam; et Baasa avait tué Jéhu.
Ban da haka, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Yehu ɗan Hanani wa Ba’asha da gidansa, saboda dukan muguntar da ya aikata a gaban Ubangiji, ya tsokane shi yă yi fushi ta wurin abubuwan da ya yi, da kuma zama kamar gidan Yerobowam, da kuma domin ya hallaka gidan Yerobowam.
8 Et Ela, fils de Baasa, régna deux ans sur Israël, à Thersa.
A shekara ta ashirin da shida ta Asa sarkin Yahuda, Ela ɗan Ba’asha ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Tirza shekaru biyu.
9 Et Zambri, chef de la moitié de sa cavalerie, se révolta contre lui; comme il était à boire, et déjà ivre, dans la maison d'Osa, son économe, à Thersa,
Zimri, ɗaya daga cikin shugabanni, wanda ya shugabanci rabin kekunan yaƙin Ela, ya yi maƙarƙashiya a kansa. Ela yana a Tirza a lokacin, ya bugu a gidan Arza, sarkin fada a Tirza.
10 Zambri entra, le frappa, le tua, et régna à sa place.
Zimri ya shiga, ya buge shi ya kashe a shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda. Sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki.
11 Et, aussitôt qu'il fut proclamé roi, et qu'il se fut assis sur le trône,
Nan da nan sai ya fara mulki ya kuwa zauna a kujerar sarauta, ya kashe dukan iyalin Ba’asha. Bai bar namiji guda ɗaya ba, ko dangi, ko aboki.
12 Il extermina toute la famille de Baasa, selon la parole qu'avait dite le Seigneur sur la maison de Baasa, par la voix de Jéhu le prophète,
Ta haka Zimri ya hallaka dukan iyalin Ba’asha, bisa ga maganar da Ubangiji ya yi game da Ba’asha ta wurin annabi Yehu.
13 Concernant les péchés de Baasa et de son fils Ela, et le péché où ils avaient fait tomber Israël, qui, par ses vanités, avait irrité le Seigneur.
Wannan ya faru saboda dukan zunuban Ba’asha da waɗanda ɗansa Ela ya yi, da ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
14 Quant au reste de l'histoire d'Ela, n'est-il pas écrit au livre des faits et gestes des rois d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Ela, da dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
15 Zambri régna sept jours à Thersa; alors, Israël était campé devant Gabathon, ville des Philistins.
A shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda, Zimri ya yi mulki a Tirza kwana bakwai. Mayaƙa suka yi sansani kusa da Gibbeton, wani garin Filistiyawa.
16 Et le peuple mût dans le camp que l'on disait: Zambri s'est révolté et il a tué le roi; aussitôt, le peuple d'Israël proclama roi Ambri, qui, ce jour-là, commandait l'armée et le camp.
Sa’ad da Isra’ilawa a cikin sansani suka ji cewa Zimri ya yi maƙarƙashiya a kan sarki, ya kuma kashe shi, sai suka yi shela, suka naɗa Omri, shugaban mayaƙa ya zama sarki a bisa Isra’ila, a wannan rana a cikin sansani.
17 Et Ambri, avec tout Israël, partit de Gabathon, et il assiégea Thersa.
Sai Omri da dukan Isra’ilawa suka janye daga Gibbeton, suka yi wa Tirza kwanto.
18 Quand Zambri vit que sa ville était prise, il se réfugia dans un souterrain de son palais; puis, il brûla sur lui le palais, et il mourut,
Da Zimri ya ga cewa an kame birnin, sai ya je ya shiga hasumiya fadan sarki ya sa wa fadan wuta wutar kuwa ta ƙone shi ya mutu.
19 A cause des péchés qu'il avait commis en faisant le mal devant le Seigneur, en faisait tomber Israël dans le péché, et en marchant dans la voie de Jéroboam.
Wannan ya faru saboda zunuban da ya yi, ya yi mugunta a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubin da Yerobowam ya yi da ya sa Isra’ila suka yi.
20 Pour le reste de l'histoire de Zambri, n'est-il pas écrit au livre des Faits et gestes des rois d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Zimri, da tawayen da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
21 Alors, le peuple d'Israël se divisa: la moitié voulut pour roi Thamni, fils de Gonath; l'autre moitié, Ambri.
Sai mutanen Isra’ila suka rabu kashi biyu; rabi guda sun goyi bayan Tibni ɗan Ginat yă zama sarki, ɗayan rabin kuma sun goyi bayan Omri.
22 Le peuple qui suivait Ambri l'emporta sur le peuple qui suivait Thamni, fils de Gonath; Thamni mourut, en ce temps-là, ainsi que Joram, son frère, et Ambri régna après Thamni.
Amma mabiyan Omri suka nuna sun fi na Tibni ɗan Ginat ƙarfi. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.
23 En la trente et unième année du règne d'Asa en Juda, Ambri fut reconnu roi d'Israël; il régna douze ans, dont six à Thersa.
A shekara ta talatin da ɗaya na Asa sarkin Yahuda, Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu, shekaru shida a Tirza.
24 Et Ambri acheta la montagne de Samarie, de Samar, qui était maître de cette montagne, au prix de deux talents d'argent; il bâtit sur la montagne une ville qu'il appela Samarie, du nom de celui qui la lui avait vendue.
Ya saya tudun Samariya daga Shemer, a bakin talentin biyu na azurfa, ya kuma gina birni a kan tudun, ya kira shi Samariya, bayan Shemer, sunan mai tudun a dā.
25 Et Ambri fit le mal devant le Seigneur; il fit le mal plus que tous ceux qui avaient régné avant lui.
Amma Omri ya yi mugunta a gaban Ubangiji, ya kuma yi zunubi fiye da dukan waɗanda suka kasance kafin shi.
26 Il marcha dans toutes les voies de Jéroboam, fils de Nabat, et dans les péchés où il avait fait tomber tout Israël qui, par ses vanités, avait irrité le Seigneur.
Ya yi tafiya a dukan hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat da kuma cikin zunubinsa wanda ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
27 Quant au reste de l'histoire d'Ambri, aux actions qu'il fit dans sa puissance, ne sont-ils pas écrits au livre des Faits et gestes des rois d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Omri, abin da ya yi, da kuma abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
28 Et Ambri s'endormit avec ses pères; il fut inhumé à Samarie, et; son fils Achab régna à sa place.
Omri ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Samariya. Sai Ahab ya gāje shi a matsayin sarki.
29 La seconde année du règne de Josaphat en Juda, Achab commença, dans Samarie, un règne de vingt-deux ans.
A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Samariya a kan Isra’ila, shekara ashirin da biyu.
30 Et Achab fit le mal devant le Seigneur; il fit le mal plus que tous ceux qui avaient régné avant lui.
Ahab ɗan Omri ya yi mugunta sosai a gaban Ubangiji fiye da wani daga cikin waɗanda suka riga shi.
31 Il ne lui suffit pas de marcher dans les péchés de Jéroboam, fils de Nabat; il prit pour femme Jézabel, fille d'Ethbaal, roi des Sidoniens; il l'imita, il servit Baal, et l'adora.
Bai zama masa wani abu mai wuya ba, yă yi zunuban Yerobowam ɗan Nebat, har ma ya auri Yezebel’yar Etba’al sarkin Sidoniyawa, ya kuma fara bauta wa Ba’al, ya yi masa sujada.
32 Et il éleva un autel à Baal dans le temple d'abomination qu'il avait bâti à Samarie.
Ya kafa bagade domin Ba’al a haikalin Ba’al da ya gina a Samariya.
33 Il planta un bois sacré, et il continua ses abominations pour irriter le Seigneur et perdre son âme. Il fit le mal plus que tous ceux qui, avant lui, avaient régné sur Israël.
Ahab ya gina ginshiƙin Ashera, ya kuma aikata abubuwa masu yawa don yă tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi fiye da dukan sarakunan Isra’ila da suka riga shi.
34 En ces jours-là, Achiel le Béthélite rebâtit Jéricho en sacrifiant son premier-né, Abiron, qui mourut comme il jetait les fondations; et Segub, le plus jeune de ses fils, qui mourut quand il posa les portes, selon la parole que le Seigneur avait dite par la voix de Josué, fils de Nau.
A lokaci Ahab ne, Hiyel mutumin Betel ya sāke gina Yeriko. Ya kafa tushensa a bakin ran ɗan farinsa Abiram, ya kuma kafa ƙofofinsa a bakin ran autansa Segub, bisa ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.

< 1 Rois 16 >