< 1 Rois 13 >

1 Or, voilà qu'un homme de Dieu vint de Juda à Béthel avec la parole du Seigneur, et Jéroboam était devant l'autel pour y sacrifier.
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
2 Et l'homme cria contre l'autel avec la parole du Seigneur, et il dit: Autel! autel! Voici ce que dit le Seigneur: Il naîtra de la maison de David un fils, son nom sera Josias; il immolera sur toi les prêtres des hauts lieux qui font pour toi des sacrifices, et il brûlera sur toi des ossements humains.
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
3 Et, ce jour même, l'homme donna un signe, et dit: Voici la parole qu'a dite le Seigneur; il a dit: Voilà que l'autel est fendu; la graisse qu'on y a déposée va se répandre à terre.
A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
4 Lorsque le roi Jéroboam eut ouï les paroles de l'homme de Dieu et ses imprécations contre l'autel, il étendit sur lui la main, et il dit: Saisissez- le. Aussitôt la main que de l'autel il avait étendue vers l'homme, se dessécha, et il ne put la ramener à lui.
Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
5 Et l'autel se fendit, et la graisse qu'on y avait déposée se répandit à terre, selon le signe que l'homme de Dieu avait donné avec la parole du Seigneur.
Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
6 Alors, le roi Jéroboam dit à l'homme de Dieu: Prie devant le Seigneur ton Dieu, que je puisse ramener ma main. L'homme de Dieu pria devant le Seigneur, et il rendit au roi l'usage de sa main, qui redevint comme auparavant.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
7 Après cela, le roi dit à l'homme de Dieu: Entre avec moi dans ma demeure, déjeune, et je te ferai des présents.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
8 Mais l'homme de Dieu dit au roi: Tu me donnerais la moitié de ta maison que je n'y entrerais pas avec toi; je ne mangerai pas de pain, je ne boirai point d'eau en ce lieu.
Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
9 Car le Seigneur, avec sa parole, m'a fait un ordre, il a dit: Ne mange pas de pain, ne bois point d'eau, et, en t'en allant, ne prends pas le chemin par où tu es venu.
Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
10 Et il s'en retourna par un autre chemin, et il ne prit point celui par où il était venu à Béthel.
Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
11 Or, il y avait à Béthel un prophète avancé en âge, et ses fils allèrent lui raconter les œuvres que, ce jour-là, l'homme de Dieu avait faites en Béthel, et les paroles qu'il avait dites au roi. Et leur père changea de visage.
To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
12 Et leur père dit: Par où s'en va-t-il? Ses fils lui montrèrent le chemin que venait de prendre l'homme de Dieu venu de Juda.
Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
13 Et il dit à ses fils: Bâtez-moi l'âne; ils lui bâtèrent son âne, et il courut après l'homme.
Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
14 Il prit le même chemin que l'homme de Dieu; et il le trouva assis sous un chêne, et il lui dit: Es-tu l'homme de Dieu venu de Juda? L'autre répliqua: Je le suis.
Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
15 Et il lui dit: Viens avec moi, et mange du pain.
Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
16 Je ne puis te suivre, reprit l'autre, ni manger du pain ni boire de l'eau en ce lieu.
Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
17 Car le Seigneur m'a donné ses ordres de sa propre bouche; il a dit: Ne mange pas là de pain, n'y bois point d'eau, et, en t'en allant, ne prends pas le chemin par où tu es venu.
An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
18 Mais le vieillard lui dit: Moi aussi je suis comme toi prophète; un ange du Seigneur m'a parlé avec la parole du Seigneur, disant: Ramène-le avec toi en ta maison; qu'il mange du pain, qu'il boive de l'eau. Or, le vieillard le trompait.
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19 Il revint donc, il mangea du pain, il but de l'eau en sa maison.
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
20 Et ceci advint: Comme ils étaient assis à table, la parole du Seigneur vint au prophète qui l'avait ramené.
Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
21 Et il dit à l'homme de Dieu qui était venu de Juda: Voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que tu as irrité la parole du Seigneur, de ce que tu n'as point gardé le commandement que t'avait fait le Seigneur ton Dieu,
Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
22 De ce que tu es revenu, de ce que tu as bu et mangé dans ce lieu, après qu'il t'avait dit: «Tu n'y mangeras pas de pain, tu n'y boiras point d'eau, » ton corps n'entrera pas dans le sépulcre de tes pères.
Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
23 Or, quand l'homme de Dieu eut mangé du pain et bu de l'eau, il bâta son âne, et s'en alla.
Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
24 Mais un lion le trouva en route, et le tua; son corps resta étendu sur le chemin; l'âne ne bougea pas, et le lion se tint auprès du corps.
Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
25 Et des hommes vinrent à passer; ils virent le cadavre gisant sur le chemin, et le lion se tenant auprès du cadavre; puis, ils entrèrent dans la ville où demeurait le vieux prophète, et ils racontèrent ce qu'ils avaient vu.
Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
26 Le vieillard l'apprit, et il s'écria: Ce doit être l'homme de Dieu qui a irrité la parole du Seigneur.
Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
27 Et il sortit, et il trouva le cadavre gisant sur le chemin, l'âne et le lion se tenant auprès du corps; et le lion n'avait point mangé le mort, et il n'avait point déchiré l'âne.
Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
28 Et il sortit, et il trouva le cadavre gisant sur le chemin, l'âne et le lion se tenant auprès du corps; et le lion n'avait point mangé le mort, et il n'avait point déchiré l'âne.
Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
29 Le prophète souleva le corps de l'homme de Dieu, le plaça sur son âne, et le ramena à la ville, afin de l'ensevelir
Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
30 Dans son propre sépulcre; et ils pleurèrent sur lui, disant: Hélas! frère.
Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
31 Après qu'ils eurent pleuré sur lui, le vieillard dit à ses fils: Quand je mourrai, ensevelissez-moi dans le sépulcre où l'homme de Dieu a été enseveli; placez-moi auprès de ses ossements, afin que mes ossements soient sauvés avec les siens.
Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
32 Car la chose qu'il a dite d'après la parole du Seigneur, concernant l'autel de Béthel et les temples des hauts lieux en Samarie, s'accomplira.
Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
33 Après ces choses, Jéroboam ne se repentit point de sa méchanceté; il continua de prendre, parmi tout le peuple, des prêtres des hauts lieux. Le premier venu put avoir la main pleine, et devenir prêtre sur les hauts lieux.
Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
34 Ce fut le péché de la maison de Jéroboam, cause de sa perte et de sa disparition de la face de la terre.
Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.

< 1 Rois 13 >