< 1 Rois 11 >
1 Et le roi Salomon aimait les femmes. Il avait sept cents femmes princesses et trois cents concubines. Il avait épousé des femmes étrangères: la fille du Pharaon, puis des Moabites, des Ammonites, des Syriennes, des Iduméennes, des Hettéennes et des Amorrhéennes,
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 Des femmes de ces peuples dont le Seigneur avait dit aux fils d'Israël: «Vous n'aurez point avec eux de commerce, ni eux avec vous, de peur qu'ils ne détournent vos cœurs vers leurs idoles.» Salomon s'était attaché à elles, il les aimait.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 Et, au temps de sa vieillesse, son cœur ne fut point parfait à l'égard du Seigneur son Dieu, comme le cœur de David, son père. Car les femmes étrangères détournèrent son cœur vers leurs dieux.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 Et, au temps de sa vieillesse, son cœur ne fut point parfait à l'égard du Seigneur son Dieu, comme le cœur de David, son père. Car les femmes étrangères détournèrent son cœur vers leurs dieux.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 Alors, Salomon bâtit un haut lieu à Chamos, idole de Moab; à leur roi, idole des fils d'Ammon,
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 Et à Astarté, abomination des Sidoniens.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 A toutes ses femmes étrangères, il accorda de sacrifier à leurs idoles et de les encenser.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 Et Salomon fit le mal devant le Seigneur; il ne suivit point le Seigneur, comme l'avait suivi David, son père.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 Et le Seigneur se courrouça contre Salomon, parce qu'il avait détourné son cœur du Seigneur Dieu d'Israël qui lui était apparu deux fois,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 Et lui avait expressément commandé de ne jamais suivre d'autres dieux, d'être attentif à faire tout ce qu'avait prescrit le Seigneur Dieu; en effet, son cœur n'était point parfait à l'égard du Seigneur, comme le cœur de David, son père.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 Et le Seigneur dit à Salomon: En punition de ce que tu as agi de la sorte et n'as point gardé mes commandements et mes ordonnances que je t'avais donnés, je déchirerai dans tes mains ton royaume, et j'en donnerai une part à ton serviteur.
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 Seulement, à cause de David, ton père, je ne ferai point ces choses de ton vivant; je retirerai des mains de ton fils cette part du royaume.
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 Car je ne le lui prendrai pas tout entier; je laisserai un sceptre à ton fils, à cause de David, mon serviteur, et à cause de Jérusalem, ville que j'ai choisie.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 Et le Seigneur avait suscité des satans contre Salomon: Ader l'Iduméen et Esron, fils d'Eliadaé de Raama, jadis serviteur d'Adadézer, roi de Suba; ils avaient rassemblé des hommes contre lui, et Ader, chef de cette troupe, avait pris Damas; il fut l'ennemi d'Israël tant que vécut Salomon, et il était de la famille des rois de l'Idumée.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Or, ceci était advenu: Dans le temps que David exterminait Edom, et que Joab, général de son armée, était à ensevelir les morts, car ils frappaient tous les mâles dans l'Idumée,
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 (Joab y passa six mois avec tout Israël, jusqu'à ce qu'ils eussent détruit tous les mâles de l'Idumée.)
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 Ader s'enfuit emmenant avec lui tous les Iduméens, serviteurs de son père; il se réfugia en Égypte, alors petit enfant;
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 Et des hommes de la ville de Madian s'étaient soulevés; quand Ader et les siens entrèrent dans Pharan, prirent avec eux les hommes, et allèrent chez le Pharaon, roi d'Égypte. Ader fut introduit auprès du Pharaon; le roi lui donna une demeure, et lui assigna des vivres.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 Et Ader trouva grâce devant le Pharaon, et le roi lui fit épouser la sœur de sa femme Thécémina, la sœur aînée de Thécémina.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 Cette sœur de Thécémina enfanta pour Ader un fils nommé Ganebath, que Thécémina éleva avec les fils du Pharaon; Ganebath était donc parmi les fils du Pharaon.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 Lorsque Ader apprit en Égypte que David dormait auprès de ses pères, et que Joab, général de son armée, était mort; il dit au Pharaon: Congédie-moi, et je retournerai dans mon pays.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 Et le Pharaon répondit à Ader: Que te manque-t-il parmi nous? Pourquoi demandes-tu à retourner en ton pays? Ader reprit: Je désire que tu me congédies. Et il revint en sa contrée.
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 Voilà d'où venait la méchanceté d'Ader, il contristait Israël et il régnait sur Edom.
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 Voilà d'où venait la méchanceté d'Ader, il contristait Israël et il régnait sur Edom.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 Voilà d'où venait la méchanceté d'Ader, il contristait Israël et il régnait sur Edom.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 Or, Jéroboam, fils de Nabat l'Ephrathéen de Sarira, fils d'une femme veuve, était serviteur de Salomon.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 Voici à quelle occasion il leva les mains contre le roi son maître. Le roi Salomon était à bâtir la citadelle, et il entourait de murs l'enceinte de la ville de David.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 Jéroboam était vaillant, et Salomon discerna que le jeune serviteur était un homme d'action, et il le nomma intendant des tributs de la maison de Joseph.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 En ce temps-là, Jéroboam sortit de Jérusalem, et il fut rencontré sur la route par Achias, le prophète silonite. Achias se détourna du chemin, et Achias était enveloppé d'un manteau neuf; ils étaient seuls tous les deux dans les champs,
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 Et Achias ôta son manteau neuf et le déchira en douze parts,
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 Et il dit à Jéroboam: Prends pour toi dix de ces lambeaux; car voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël: Je déchirerai entre les mains de Salomon son royaume, et je te donnerai dix tribus.
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 Et il lui restera deux tribus, à cause de mon serviteur David, et à cause de Jérusalem, ville que j'ai choisie parmi toutes les tribus d'Israël.
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 C'est en punition de ce qu'il m'a abandonné; de ce qu'il a sacrifié à Astarté, abomination des Sidoniens, à Chamos, aux idoles de Moab et à leur roi, abomination des fils d'Ammon, et de ce qu'il n'a point marché en toutes mes voies pour faire devant moi ce qui est droit, comme l'a fait David, son père.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Toutefois, je ne retirerai point de sa main le royaume entier; je le lui laisserai même tout le reste de sa vie, à cause de David, son père, mon élu.
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 Mais je prendrai le royaume des mains de son fils, et je te donnerai dix tribus.
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 Et je laisserai à son fils deux tribus, afin qu'il y ait toujours devant moi, pour mon serviteur David, un trône en Jérusalem, dans la ville que je me suis choisie pour que mon nom y résidât.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 Pour toi, je te prendrai, et tu règneras comme le désire ton âme; tu seras roi d'Israël.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 Et, si tu observes tout ce que je t'ordonnerai, si tu marches en mes voies, si tu fais devant moi ce qui est droit, en gardant mes commandements et mes ordonnances, comme a fait David, mon serviteur, je serai avec toi, et je te bâtirai une maison sûre, de même que j'en ai bâti une pour David.
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 Et Salomon chercha à faire périr Jéroboam; mais il partit, et s'enfuit auprès de Sésac, roi d'Égypte, et il y demeura jusqu'à la mort de Salomon.
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Et Salomon chercha à faire périr Jéroboam; mais il partit, et s'enfuit auprès de Sésac, roi d'Égypte, et il y demeura jusqu'à la mort de Salomon.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 Le reste de l'histoire de Salomon, tout ce qu'il a fait, toute sa sagesse, ne sont-ils pas écrits au livre de la vie de Salomon?
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 Salomon régna quarante ans sur tout Israël.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 Et il s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit en la ville de David, et Roboam, son fils, régnait à sa place.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.