< 1 Chroniques 5 >

1 Voici les fils de Ruben; il était le premier-né; mais parce qu'il s'était introduit dans la couche de son père, Jacob ayant donné sa bénédiction à son fils Joseph, le droit d'aînesse de Ruben ne lui était plus compté.
’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
2 Car Juda était fort parmi ses frères; le chef est sorti de lui, la bénédiction est restée à Joseph.
ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
3 Fils de Ruben, premier-né d'Israël: Enoch, Phallus, Asron et Charmi.
’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
4 Fils de Johel: Sémeï et Banaïas son fils. Fils de Gug, fils de Sémeï,
Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
5 Micha, son fils Recha, son fils Johel,
Mika, Reyahiya, Ba’al,
6 Son fils Behel, qu'emmena Thelgath-Phalnasar, roi des Assyriens; il était le chef des Rubénites.
da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
7 Et, avec lui, furent emmenés ses frères, selon le dénombrement qui en fut fait par familles; les chefs de ces familles étaient: Johel, Zacharie,
Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
8 Et Balec, fils d'Azuz, fils de Sama, fils de Johel. Balec demeurait en Aroer, et vers Nebo et Belmasson.
da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
9 Et il s'était étendu à l'orient jusqu'au désert, du côté de l'Euphrate, parce qu'il avait de nombreux troupeaux en la terre de Galaad.
Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
10 Et, sous le règne de Saül, ils furent en guerre avec leurs voisins, et ceux qui habitaient sous des tentes tombèrent entre leurs mains, et ils maîtrisèrent toute la contrée à l'orient de Galaad.
A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
11 Les fils de Gad, en face, demeurèrent en la terre de Basan jusqu'à Sela.
Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
12 Le premier-né fut Johel; le second Saphan; puis, venaient Jania, le scribe de Basan,
Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
13 Et ses frères, par familles paternelles: Michel, Mosollam, Sébée, Joré, Joachan, Zué et Obed; sept.
Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
14 Les fils d'Abihaïl, fils d'Uri, fils d'Isaïe, fils de Galaad, fils de Michel, fils de Jésé, fils de Jeddé, fils de Bas,
Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
15 Frère du fils d'Abdiel, fils de Guni, chef de la maison paternelle,
Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
16 Habitaient en Galaad, en Basan, en leurs bourgs et en tout le territoire de Saron jusqu'à ses limites.
Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
17 Leur dénombrement fut fait du temps de Joatham, roi de Juda, et de Jéroboam, roi d'Israël.
Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
18 Les fils de Ruben, Gad et la demi-tribu de Manassé comptaient quarante- quatre mille sept cent soixante hommes, dans la force de l'âge, portant glaive et bouclier, tendant l'arc, exercés à la guerre, propres à marcher au combat.
Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
19 Et ils furent en guerre avec les Agaréens, les Ituréens, les Naphiséens et les Nadabéens.
Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
20 Et ils l'emportèrent sur eux. Et les Agaréens, avec toutes leurs tentes, tombèrent entre leurs mains, parce que les vainqueurs avaient invoqué Dieu pendant la bataille; et Dieu les exauça, parce qu'ils avaient espéré en lui.
Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
21 Et ils prirent tout ce que les autres possédaient: cinquante mille chameaux, deux cent cinquante mille brebis, deux mille ânes; et la vie de cent mille hommes.
Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
22 Car une grande multitude de blessés succomba, parce que cette guerre s'était faite selon la volonté de Dieu, et les vainqueurs habitèrent le territoire des vaincus Jusqu'à la captivité.
waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
23 Et la demi-tribu de Manassé s'étendit de Basan Baal, Hermon, Sanir et la montagne d'Hermon; ses fils se multiplièrent dans le Liban.
Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
24 Et voici leurs chefs, par familles: Opher, Sei, Eliel, Jérémie, Oduïa et Jediel; hommes riches et renommés, chefs des familles de la demi-tribu.
Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
25 Et ils répudièrent le Dieu de leurs pères, et ils se prostituèrent à la suite des dieux de la terre que le Seigneur avait effacés devant leur face.
Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
26 Et le Dieu d'Israël excita l'esprit de Phaloch (Phul), roi d'Assur, et l'esprit de Thelgath-Phalnasar, roi d'Assur. Ce roi enleva Ruben, et Gad, et la demi-tribu de Manassé, et il les transporta en Haach, en Hahor, et sur le fleuve Gozan, où ils sont restés jusqu'à nos jours.
Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.

< 1 Chroniques 5 >