< 1 Chroniques 29 >
1 Et le roi David dit à toute l'Église: Mon fils Salomon, en qui le Seigneur s'est complu, est jeune et délicat, et l'œuvre est grande, car elle n'est point pour l'homme, mais pour le Seigneur Dieu.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 Autant que je l'ai pu, j'ai préparé pour le temple de mon Dieu: de l'or, de l'argent, de l'airain, du fer, des bois, des pierres d'onyx, quantité de pierres chères et variées, toutes sortes de pierres précieuses, et beaucoup de marbre.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 De plus, comme je mets ma joie en la demeure de mon Dieu, j'ai conservé l'or et l'argent que je me suis procuré pour moi-même; je le donne entièrement au temple de mon Dieu, outre ce que j'ai amassé pour la maison des choses saintes, savoir:
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 Trois mille talents d'or d'Ophir, et sept mille talents d'argent pur, pour que l'on en recouvre les murs du lieu saint.
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 Il y aura ce qu'il faut à la main de l'artisan. Mais est-il quelqu'un qui désire aujourd'hui remplir ses mains pour le Seigneur?
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Et les princes des familles le désirèrent, les princes des fils d'Israël ainsi que les commandants de mille hommes, et les centeniers, et les intendants des travaux, et les architectes du roi.
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 Et ils donnèrent pour les travaux du temple du Seigneur: cinq mille talents et dix mille sicles d'or; dix mille talents d'argent; dix-huit mille talents d'airain et cent mille talents de fer.
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 Et celui chez qui il se trouva quelque pierre précieuse, la donna pour le trésor du temple par les mains de Dehiel, de la famille de Gerson.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Et le peuple eut une grande joie à cause de ce zèle, car chacun eut ce zèle pour Dieu de plein cœur. Et le roi David fut comblé de joie.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 Et le roi David bénit le Seigneur devant toute l'Église, disant: Béni soyez-vous, Seigneur Dieu d'Israël, ô notre Père, dans tous les siècles des siècles!
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 A vous, Seigneur, la magnificence, la force, la gloire, la victoire et la puissance; car vous êtes le maître de toutes les choses qui sont sur la terre et dans les cieux. Tous les rois des nations sont troublés devant vous.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 De vous viennent gloire et richesse; vous régnez sur toutes choses, ô Seigneur, prince de toutes les dominations; la force et le pouvoir résident en vos mains, et il dépend de vous, ô Tout-Puissant, de grandir et de fortifier toutes choses.
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 Et maintenant, Seigneur, nous vous rendons hommage, nous louons votre nom et votre gloire.
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 Et qui suis-je, moi, et qui est mon peuple, pour que nous ayons pu vous faire ces offrandes avec tant de zèle? Tout est à vous, et nous vous avons donné de ce qui vous appartient.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 Car nous sommes des passagers devant vous, et Nous passons comme tous nos pères; nos jours sur la terre sont comme l'ombre, et rien n'a de la durée.
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 Seigneur notre Dieu, toutes les richesses que j'ai préparées pour bâtir un temple à votre saint nom, viennent de vous; tout cela vous appartient.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 Et j'ai reconnu, ô mon Dieu, que c'est vous qui sondez les cœurs et que vous aimez la justice; et je vous ai fait mes offrandes dans la simplicité de mon cœur, et je viens de voir ici avec joie ce peuple mettre tant de zèle à vous faire ses offrandes.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 Seigneur Dieu d'Abraham, d'Isaac et d'Israël nos pères, faites que votre peuple conserve toujours en son cœur le même amour, et dirigez son cœur vers vous.
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 Et donnez à mon fils Salomon un bon cœur pour exécuter vos commandements, pour être attentif à vos ordres et à vos témoignages, et pour conduire jusqu'à la fin la construction de votre temple.
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 Et David dit à toute l'Église: Bénissez le Seigneur notre Dieu. Et toute l'Église bénit le Seigneur Dieu de leurs pères; ils plièrent les genoux et ils adorèrent le Seigneur et le roi.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 Et David sacrifia au Seigneur; il offrit en holocauste à Dieu, dès le matin du jour suivant: mille bœufs, mille béliers, mille agneaux; il fit leurs libations, et il distribua des victimes en abondance à tout Israël.
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 Et ils mangèrent, et ils burent avec joie devant le Seigneur toute la journée, et, pour la seconde fois, ils proclamèrent roi Salomon, fils de David; ils le sacrèrent roi devant le Seigneur, et ils sacrèrent Sadoc comme pontife.
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 Et Salomon s'assit sur le trône de David son père; il fut honoré, et tout Israël lui obéit.
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 Les princes, les vaillants, et tous les fils du roi David son père, se soumirent à sa puissance.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 Et le Seigneur éleva Salomon au-dessus de tout Israël, il lui donna plus de gloire qu'à nul des rois qui l'avaient devancé.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 Or, David, fils de Jessé, avait régné sur Israël
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 Quarante ans: sept à Hébron, trente-trois à Jérusalem.
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 Et il finit en une heureuse vieillesse, plein de jours, de richesses et de gloire, et son fils Salomon régna à sa place.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Le reste des discours du roi David, ses premières et ses dernières paroles, sont écrits parmi les Récits de Samuel le voyant, de Nathan le prophète, et de Gad le voyant,
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 Concernant tout son règne, ses guerres et les événements arrivés tant à lui qu'à Israël, et en tous les royaumes de la terre.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.