< 1 Chroniques 16 >

1 Et ils introduisirent l'arche de Dieu, et la placèrent au milieu du tabernacle que David avait dressé pour elle, et l'on offrit devant Dieu des holocaustes et des hosties pacifiques.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 Quand David eut fait ses offrandes d'holocaustes et d'hosties pacifiques, il bénit le peuple au nom du Seigneur.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 Et il donna à chaque homme et à chaque femme d'Israël un pain de boulanger, et un pain pétri avec du miel.
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 Et il institua devant l'arche de l'alliance du Seigneur ceux des lévites qui devaient y être employés, pour chanter et louer le Seigneur Dieu d'Israël, et lui rendre grâces.
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph fut le chef, et il eut pour second Zacharie; puis, Jehiel, Semiramoth et Jehiel, Matthathias, Eliab, Banaïas et Abdedom: Jehiel jouait de la lyre et de la harpe, et Asaph faisait retentir des cymbales.
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 Banaïas et Oziel les prêtres, sonnaient toujours de la trompette devant l'arche de l'alliance du Seigneur.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Et ce jour-là, pour la première fois, David prescrivit que l'on chantât les louanges du Seigneur, sous la direction d'Asaph et de ses frères.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 Cantique. Rendez hommage au Seigneur, invoquez-le par son nom, faites connaître aux peuples ses désirs.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Chantez-le, chantez ses louanges; racontez à tous les merveilles qu'a faites le Seigneur.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Louez son saint nom; le cœur qui cherche à lui âtre agréable sera réjoui.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Cherchez le Seigneur et soyez forts; cherchez toujours son visage.
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Souvenez-vous des prodiges qu'il a faits, des merveilles et des jugements sortis de sa bouche.
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 Enfants d'Israël, ses serviteurs; fils de Jacob, ses élus;
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 Le Seigneur seul est notre Dieu; ses jugements sont sur toute la terre.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Souvenons-nous toujours de son alliance, de la loi qu'il nous a donnée pour des milliers de générations,
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 De son alliance avec Abraham; de son serment à Isaac,
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 Il l'a confirmé à Jacob comme un commandement, à Israël comme une alliance impérissable,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 Disant: Je te donnerai la terre de Chanaan; c'est ta part d'héritage.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 Alors, ils étaient en petit nombre, ils étaient humbles, et ils étaient passagers sur cette terre,
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 Et ils allèrent d'une nation à l'autre, et d'un royaume à un autre peuple,
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 Et à nul homme il ne permit de prévaloir sur eux, et à leur sujet il châtia des rois:
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 Ne touchez point à mes christs; ne maltraitez pas mes prophètes,
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Chantez le Seigneur: que toute la terre le chante, proclamez chaque jour que lui seul est notre salut.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 [Racontez aux nations sa gloire, à tous les peuples ses merveilles.] Car le Seigneur est grand et digne de louanges infinies; il est redoutable plus que tous les dieux.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 [Racontez aux nations sa gloire, à tous les peuples ses merveilles.] Car le Seigneur est grand et digne de louanges infinies; il est redoutable plus que tous les dieux.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 Car, tous les dieux des nations sont des idoles, et notre Dieu a créé le ciel.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 Gloire et louange à lui face à face; force et joie au lieu où il réside.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Tribus des nations, donnez au Seigneur, donnez au Seigneur force et gloire.
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Glorifiez le nom du Seigneur; prenez des dons et offrez-les au Seigneur en sa présence, et adorez le Seigneur dans ses demeures saintes.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Que toute la terre ait crainte devant lui; que la terre s'affermisse et ne soit point ébranlée.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Que le ciel se réjouisse, que la terre tressaille d'allégresse, et qu'ils disent aux nations: Le Seigneur règne.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 La mer bruira dans sa plénitude, et l'arbre des champs avec tout ce qu'il porte se réjouira.
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Alors, les arbres de la forêt se réjouiront devant le Seigneur, parce qu'il est venu juger la terre.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 Rendez hommage au Seigneur, parce qu'il est bon et que sa miséricorde est éternelle.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 Et dites: Sauvez-nous, ô Dieu notre salut; recueillez-nous et séparez- nous des nations, afin que nous chantions les louanges de votre saint nom, et que noua mettions notre gloire à vous louer.
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Béni soit le nom du Seigneur Dieu d'Israël dans tous les siècles des siècles, et tout le peuple dira: Amen. Et ils louèrent le Seigneur.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 Et ils laissèrent là devant l'arche de l'alliance du Seigneur Asaph et ses frères, pour faire devant l'arche à perpétuité le service de chaque jour.
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 Ils laissèrent aussi Abdedom et ses frères, au nombre de soixante-huit, et Abdedom, fils d'Idithun, et Osa pour être portiers.
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 Et Sadoc le prêtre, avec ses frères les prêtres, fut laissé devant le tabernacle du Seigneur, sur le haut lieu de Gabaon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 Afin d'offrir des holocaustes au Seigneur, sur l'autel des holocaustes à perpétuité, matin et soir, selon qu'il est écrit en la loi du Seigneur, qu'il a donnée aux fils d'Israël par la voix de Moïse, son serviteur.
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 Et avec Sadoc étaient Hêman et Idithun, et le reste de ceux qu'on avait nominativement désignés pour louer le Seigneur, parce que sa miséricorde est éternelle.
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 Et ils avaient avec eux des trompettes et des cymbales, pour les faire retentir, et les instruments accompagnant les cantiques de Dieu. Et les fils d'Idithun étaient gardiens des portes.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 Et le peuple s'en retourna chacun en sa demeure, et David s'en alla pour bénir sa maison.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.

< 1 Chroniques 16 >