< 1 Chroniques 13 >

1 Et David tint conseil avec tous ses chefs, centeniers ou commandants de mille hommes.
Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
2 Et David dit à toute l'Église d'Israël: Si cela vous paraît bon et agréable au Seigneur notre Dieu, envoyons chez nos frères qui sont restés en tout le territoire d'Israël, et chez les prêtres et les lévites, dans les villes où ils résident; qu'il se réunissent à nous,
Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
3 Et amenons auprès de nous l'arche de notre Dieu; car, depuis l'avènement de Saül, on ne l'a point demandée.
Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
4 Et toute l'Église dit qu'il fallait faire ainsi; car ce discours avait plu à tout le peuple.
Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
5 Et David réunit tout Israël, depuis les confins de l'Égypte jusqu'aux défilés d'Emath, pour ramener l'arche de la ville d'Iarim.
Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
6 Et David la ramena; et tout Israël entra dans la ville de David, qui est en Juda, pour y introduire l'arche du Seigneur Dieu assis sur les chérubins, où est invoqué son nom.
Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
7 On avait posé l'arche de Dieu sur un chariot neuf de la maison d'Aminadab; Oza et ses frères conduisaient l'attelage.
Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
8 Et David et tout Israël jouaient de tout leur cœur de la flûte, de la lyre, du tambour, et des cymbales, et de la harpe, au milieu des cantiques.
Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
9 Et ils vinrent jusqu'à l'aire; là, Oza étendit la main pour maintenir l'arche que le mouvement d'un bœuf avait fait pencher.
Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
10 Mais le Seigneur s'irrita contre Oza, et il le frappa en ce lieu même, parce qu'il avait porté la main sur l'arche; et il mourut là devant Dieu.
Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
11 Et David fut abattu, parce que Dieu avait châtié Oza, et ce lieu fut appelé le Châtiment d'Oza, nom qu'il porte encore de nos jours.
Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
12 Et, ce jour-là, David eut crainte du Seigneur, et il dit: Comment ferai- je entrer chez moi l'arche du Seigneur?
Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
13 Et David ne ramena pas l'arche avec lui dans la ville de David; mais la fit placer en la maison d'Abdara le Géthéen.
Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
14 Et l'arche du Seigneur resta trois mois en la maison d'Abdara le Géthéen, et le Seigneur bénit toute la maison d'Abdara et tout ce qui lui appartenait.
Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.

< 1 Chroniques 13 >