< 1 Chroniques 12 >
1 Et voici ceux qui accompagnaient David à Sicelag, quand il était contraint de se cacher de Saül, fils de Cis; et ils comptaient parmi les vaillants, hommes de secours dans les batailles.
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 Ils tiraient leur arc de la main droite et de la main gauche; ils étaient frondeurs et archers. Des frères de Saül, de la tribu de Benjamin,
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 Le chef était Achiézer; puis, venaient Joas, fils d'Asma le Gabathéen; Johel, Jophalet, fils d'Asmoth; Berchia, Jehul d'Anathoth,
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 Samaïas de Gabaon, vaillant parmi les trente, et leur chef, puis, Jérémie, Jézéel, Joanan, Joazobath de Garathiim,
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Azaï, Arimuth, Baalie, Samaraie et Saphatias d'Haréphiel,
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Elcana, Jesuni, Ozriel, Jozara, Sobocam et les Coréens,
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 Et Jelia, Zabadie, fils de Joram, et ceux de Gédor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 Et, de la tribu de Gad, des hommes vaillants et forts, quittant le désert, rejoignirent David; tous exercés aux combats, portant bouclier et javelines, hommes à face de lion, et légers à la course dans les montagnes, comme des chevreuils.
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Aza était le chef, Abdias le second, Eliab le troisième,
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Masmana le quatrième, Jérémie le cinquième,
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Jéthi le sixième, Eliab le septième,
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Joanan le huitième, Eléazer le neuvième,
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jérémia le dixième, Melcbanaï le onzième.
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 Ils étaient les chefs de l'armée des fils de Gad; celui du moindre rang commandait cent hommes; celui du rang le plus élevé en commandait mille.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 Ce furent ceux-là qui passèrent le Jourdain pendant le premier mois, lorsqu'il coulait à pleins bords, et ils mirent en fuite tous ceux qui habitaient ses deux rives.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 Il vint aussi à David des auxiliaires des fils de Benjamin et de Juda.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 Et David se porta au-devant d'eux, et il leur dit: Si vous êtes venus en paix, mon cœur sera bienveillant pour vous; mais si vous n'êtes point sincères, si vous avez dessein de me livrer à mes ennemis, que le Dieu de vos pères vous voie, et qu'il vous punisse.
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 Et l'esprit entra en Amasaï, un chef des trente, et il dit: David, fils de Jessé, marche avec ton peuple, la paix, la paix avec toi, la paix avec tes auxiliaires; car c'est ton Dieu qui t'a secondé. Et David les accueillit, et il leur donna des commandements dans l'armée.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 Et des fils de Manassé vinrent à David, dans le même temps que les Philistins étaient en guerre avec Saül, et qu'ils avaient répudié le secours de David, parce que, dans leur conseil, les chefs des Philistins avaient dit: Il se réconciliera avec son maître Saül, en lui portant les têtes de nos hommes.
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 Et comme il retournait à Sicelag, Edna, Josabeth, Rodiel, Michel, Josabeth, Elimuth et Semathi, vinrent auprès de lui, de Manassé; c'étaient des chefs de mille hommes de Manassé.
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 Et ils furent les auxiliaires de David contre ses ennemis; tous vaillants, comme ils l'étaient, prirent rang parmi les chefs de l'armée.
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 Car cette armée s'augmentait de jour en jour, et elle devenait forte comme l'armée de Dieu.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 Et voici le dénombrement des chefs de l'armée qui entrèrent avec David à Hébron, pour lui transmettre la royauté de Saül, selon la parole du Seigneur.
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 Fils de Juda, portant lance et bouclier: six mille huit cents, prêts à combattre.
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 Fils de Siméon, vaillants prêts à combattre: sept mille cent.
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 Fils de Lévi: quatre mille six cents.
mutanen Lawi, su 4,600,
27 Joad conduisait les fils d'Aaron; il avait avec lui trois mille sept cents hommes.
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 Sadoc, jeune homme fort et vaillant, avait amené, de sa famille paternelle, vingt-deux chefs.
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 Fils de Benjamin, frères de Saül: trois mille; mais le plus grand nombre de cette tribu formait encore la garde du palais de Saül.
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 Fils d'Ephraïm: vingt mille, vaillants et forts, hommes illustres dans leurs familles paternelles.
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 Fils de la demi-tribu de Manassé: dix-huit mille, qui furent recensés nominativement, pour établir roi David.
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 Fils d'Issachar, connaissant ce qu'exigeaient les circonstances, sachant ce qu'il y avait à faire pour Israël: deux cents, et avec eux tous leurs frères.
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 Fils de Zabulon, allant au combat avec toutes les armes de guerre: cinquante mille, auxiliaires de David, n'ayant pas les mains vides.
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 Fils de Nephthali: mille chefs, et avec eux trente-sept mille hommes, portant lance et bouclier.
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 Fils de Dan, prêts à combattre: vingt-huit mille huit cents.
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 Fils d'Aser: quarante mille auxiliaires.
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 Fils de Ruben, de Gad, et de la demi-tribu de Manassé, au delà du Jourdain, portant toutes les armes de guerre: cent vingt mille.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 Tous ces hommes, qui étaient aguerris et prêts à combattre, vinrent à Hébron, pleins d'un esprit pacifique, afin de proclamer David roi de tout Israël, et tout le reste du peuple n'avait qu'une âme pour couronner David.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 Et ils demeurèrent trois jours, mangeant et buvant ce que leurs frères avaient préparé pour eux,
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 Et ce qu'on leur apportait de tout le territoire depuis Issachar jusqu'à Zabulon et Nephthali, sur des chameaux, des ânes, des mulets et des bœufs, savoir: des viandes cuites, de la farine, des figues, des raisins secs, du vin et de l'huile, outre une multitude de bœufs et de moutons; car tout Israël était en joie.
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.