< Sophonie 1 >

1 Parole de l’Eternel, qui fut adressée à Cephania, fils de Couchi, fils de Ghedalia, fils d’Amaria, fils de Hizkia sous le règne de Josias, fils d’Amon, roi de Juda:
Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 "Je vais tout balayer de dessus la face de la terre, dit le Seigneur.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 Je vais balayer hommes et bêtes, je vais balayer oiseaux du ciel et poissons de la mer, les occasions de chute avec les impies: j’exterminerai les hommes de dessus le sol, dit le Seigneur.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 Puis j’étendrai la main sur Juda et sur tous les habitants de Jérusalem, et je ferai disparaître de cette ville ce qui reste de Baal, le nom des desservants d’idoles avec les prêtres;
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 de même ceux qui, sur les terrasses, se prosternent à l’armée céleste, qui se prosternent tantôt en jurant par l’Eternel, tantôt en jurant par Malcom;
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 en outre, ceux qui se sont détournés de l’Eternel, qui ne se mettent pas en quête de lui et ne le consultent pas.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Qu’on fasse silence devant le Seigneur Dieu! Car il est proche, le jour de l’Eternel, car l’Eternel a préparé une hécatombe, il a désigné ses invités!
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 Au jour de l’hécatombe de l’Eternel, je sévirai contre les grands et les princes royaux, contre tous ceux qui endossent des vêtements étrangers.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 Je sévirai, en ce même jour, contre ceux qui sautent par-dessus le seuil des temples, et remplissent la maison de leur Maître de rapines et de fraude.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 Il y aura ce jour-là, dit l’Eternel, des cris retentissants du côté de la porte aux Poissons, des hurlements du côté du Deuxième district et un grand fracas du côté des collines.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Lamentez-vous, habitants du Makhtêch, car c’en est fait de toute cette population de marchands, ils sont perdus, tous ces gens chargés d’argent.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 En ce temps-là, j’inspecterai Jérusalem avec des lampes, et je frapperai tous ces hommes qui demeurent accroupis sur leur lie, disant en leur cœur: "L’Eternel ne peut faire du bien ni causer de dommage."
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 Leurs richesses seront mises au pillage, leurs demeures ruinées. Ils bâtiront des maisons qu’ils n’habiteront point, planteront des vignes dont ils ne boiront pas le vin.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 Il est proche, le grand jour de l’Eternel! II est proche et vient avec une extrême vitesse. Déjà on entend le bruit du jour de l’Eternel, c’est alors que le guerrier poussera des cris stridents.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 Ce jour sera un jour de colère, un jour de détresse et d’angoisse, un jour de ruine et de dévastation, un jour d’obscurité et de profondes ténèbres, un jour de nuages et de brume épaisse;
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 un jour de trompette et de fanfare guerrière contre les villes fortes et les tours élevées.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 Je serrerai de près les hommes, ils marcheront comme des aveugles, pour avoir péché contre l’Eternel. Leur sang sera répandu comme la poussière, leur sève comme des ordures.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Ni leur argent, ni leur or ne pourront les sauver au jour de la colère de l’Eternel; tout ce pays sera consumé par le feu de son indignation, car il amènera la ruine totale, la perte soudaine de tous les habitants du pays."
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Sophonie 1 >