< Sophonie 2 >

1 Recueillez-vous, tâchez de vous ressaisir, ô gens sans vergogne!
Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
2 N’Attendez pas l’échéance du terme fatal, du jour qui s’envolera rapide comme le chaume; n’attendez pas que fonde sur vous l’ardente colère du Seigneur, que vous surprenne le jour du courroux divin.
kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
3 Recherchez l’Eternel, vous tous, les humbles du pays, qui mettez en pratique ses lois. Exercez-vous à la droiture, exercez-vous à l’humilité, peut-être serez-vous à l’abri au jour de la colère de l’Eternel,
Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
4 alors que Gaza deviendra une solitude, Ascalon une ruine, alors qu’Asdod se verra expulsée en plein midi, Ekron renversée de fond en comble.
Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
5 Malheur à vous, qui occupez le littoral de la mer, peuple de Keréthites! A vous, Canaan, pays des Philistins, s’adresse la menace de l’Eternel: "Je vous ruinerai jusqu’à vous dépeupler!"
Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
6 Le district du littoral sera un lieu de pâturage percé de citernes par les bergers et un cantonnement pour les brebis.
Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
7 Ce district va échoir aux survivants de la maison de Juda, qui y pâtureront, qui, le soir venu, gîteront dans les habitations d’Ascalon, quand l’Eternel, leur Dieu, se souvenant d’eux, les aura ramenés de captivité.
Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
8 J’Avais entendu les propos outrageants de Moab, les insultes des fils d’Ammon, qui bafouaient mon peuple et manifestaient leur arrogance contre ses frontières.
“Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
9 C’Est pourquoi, dit l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël, aussi vrai que je vis, Moab sera comme Sodome, les fils d’Ammon comme Gomorrhe: un fouillis de broussailles: une mine de sel et une solitude éternelle. Les survivants de mon peuple les mettront au pillage, le reste de ma nation en prendra possession.
Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
10 Voilà ce qui leur adviendra à cause de leur orgueil, parce qu’ils ont outragé et regardé de haut le peuple de l’Eternel-Cebaot.
Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
11 L’Eternel se fera redouter d’eux, quand il réduira à rien toutes les divinités de la terre: alors toutes les îles des nations lui rendront hommage, chacune de son côté.
Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
12 Vous aussi, Couchites, vous tomberez victimes de mon glaive.
“Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
13 Puis il étendra la main sur le Nord et détruira Achour; de Ninive il fera une solitude, une lande aride comme le désert.
Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
14 Là, les troupeaux auront leur gîte, les bêtes de toute provenance; tant le pélican que le hibou éliront domicile sur ses chapiteaux. Des voix gazouilleront à travers les fenêtres, les seuils ne seront que décombres, car on aura arraché les lambris de cèdres.
Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
15 La voilà cette cité joyeuse qui trônait en pleine sécurité et disait à part soi: "Moi et personne que moi!" Ah! comme elle est devenue une solitude, un repaire de fauves! Quiconque passe près d’elle ricane et agite la main.
Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.

< Sophonie 2 >