< Zacharie 12 >
1 Enoncé de la parole de l’Eternel concernant Israël: Parole de l’Eternel qui a déployé les cieux, fondé la terre et formé l’esprit qui anime l’homme:
Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
2 "Voici que je vais faire de Jérusalem une amphore donnant le vertige à tous les peuples d’alentour; même pour ce qui est de Juda, il sera là quand Jérusalem sera serrée de près.
“Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
3 En ce jour, je ferai de Jérusalem une pierre lourde à soulever pour toutes les nations; tous ceux qui voudront la soulever s’écorcheront cruellement. Cependant tous les peuples de la terre se réuniront contre elle.
A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
4 En ce jour, dit l’Eternel, je frapperai tous les chevaux d’épouvante et leurs cavaliers de démence; mais sur la maison de Juda j’aurai les yeux ouverts, tandis que je frapperai de cécité tous les chevaux des nations.
A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
5 Alors les chefs de Juda diront en leur cœur: "Je vais renforcer le courage des habitants de Jérusalem par l’Eternel-Cebaot, leur Dieu."
Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
6 En ce jour, je ferai des chefs de Juda comme un brasier allumé parmi du bois, comme une torche enflammée au milieu d’un tas de gerbes; ils dévoreront, à droite; à gauche, toutes les nations environnantes; mais Jérusalem continuera à être solidement assise dans Jérusalem.
“A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
7 Et tout d’abord l’Eternel viendra au secours des tentes de Juda, pour que la gloire de la maison de David et la gloire des habitants de Jérusalem ne s’élèvent pas trop au-dessus de Juda.
“Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
8 En ce jour, l’Eternel étendra sa protection sur les habitants de Jérusalem, et alors le plus vacillant parmi eux sera comme David, et ceux de la maison de David paraîtront à leurs yeux comme des êtres divins, comme des anges de l’Eternel.
A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
9 En ce jour, je m’appliquerai à détruire toutes les nations venues contre Jérusalem.
A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
10 Mais sur la maison de David et sur les habitants de Jérusalem je répandrai un esprit de bienveillance et de pitié, et ils porteront les regards vers moi à cause de celui qui aura été percé de leurs coups, ils le regretteront comme on regrette un fils unique, et le pleureront amèrement comme on pleure un premier-né.
“Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
11 En ce jour, il y aura grand deuil à Jérusalem, comme fut le deuil de Hadad-Rimôn dans la vallée de Meghiddôn.
A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
12 Et le pays sera en deuil, chaque famille à part, la famille de la maison de David à part et leurs femmes à part, la famille de la maison de Nathan à part et leurs femmes à part,
Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
13 la famille de la maison de Lévi à part et leurs femmes à part, la famille de Séméi à part et leurs femmes à part,
iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
14 de même toutes les familles restantes, chaque famille à part et leurs femmes à part.
dukan sauran iyalan kuma da matansu.