< Psaumes 92 >
1 Psaume. Cantique pour le jour du Sabbat. Il est beau de rendre grâce à l’Eternel, de chanter en l’honneur de ton nom, ô Dieu suprême,
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 d’annoncer, dès le matin, ta bonté, et ta bienveillance pendant les nuits,
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 avec la lyre à dix cordes et le luth, aux sons harmonieux de la harpe.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Car tu me combles de joie, ô Eternel, par tes hauts faits; je veux célébrer les œuvres de tes mains.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 Qu’elles sont grandes tes œuvres, ô Eternel, infiniment profondes tes pensées!
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 L’Homme dépourvu de sens ne peut savoir, le sot ne peut s’en rendre compte:
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 si les méchants croissent comme l’herbe, et que fleurissent tous les artisans d’iniquité, c’est pour encourir une ruine irréparable.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 Mais toi, Seigneur, tu es éternellement sublime;
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 car voilà que tes ennemis, ô Eternel, voilà que tes ennemis succombent, que se disloquent tous les ouvriers du mal,
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 tandis que tu grandis ma force comme celle du reêm, et que ma décrépitude reverdit au contact de l’huile.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Avec satisfaction, mes yeux contemplent mes ennemis, mes oreilles entendent les malfaiteurs se dresser contre moi.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 Le juste fleurit comme le palmier; comme le cèdre du Liban, il est élancé.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Plantés dans la maison de l’Eternel, ils sont florissants dans les parvis de notre Dieu.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Jusque dans la haute vieillesse, ils donnent des fruits, ils sont pleins de sève et de verdeur,
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 prêts à proclamer que l’Eternel est droit, qu’il est mon rocher, inaccessible à l’injustice.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”