< Psaumes 73 >
1 Psaume d’Assaph. Ah! Dieu est bon pour Israël, pour ceux qui ont le cœur pur.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 Pour moi, cependant, peu s’en faut que mes pieds n’aient bronché; pour un rien, mes pas auraient glissé.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 Car je portais envie aux insensés: je voyais le bonheur des méchants.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 En effet, ils sont à l’abri de ces coups qui amènent la mort, et leur force demeure intacte.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 Ils n’ont pas leur part des misères humaines, ne subissent point les maux qui atteignent les autres.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Aussi sont-ils bouffis d’orgueil, et se drapent-ils dans leur violence comme dans un manteau.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Leurs yeux brillent à travers la graisse; les fantaisies de leur cœur dépassent toute borne.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 Ils ricanent et se targuent méchamment de tyrannie; ils parlent du haut de leur grandeur.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 Leur bouche s’attaque au ciel, leur langue promène ses ravages sur la terre.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 C’Est pourquoi son peuple en arrive au même point, et il absorbe de larges rasades d’eau,
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 tout en disant: "Comment le Tout-Puissant peut-il savoir? Le Dieu suprême possède-t-il la science?"
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Voyez ces méchants! Eternellement en sécurité, ils voient croître leur puissance.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 C’Est donc en vain que j’ai gardé mon cœur pur, et lavé mes mains pour qu’elles fussent sans tache:
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 je suis frappé sans relâche, ma peine se renouvelle chaque matin.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 Si je me fusse décidé à redire tout cela, certes j’aurais commis une trahison contre toute une génération de tes enfants.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 Je me mis donc à réfléchir pour comprendre la chose: ce fut une tâche pénible à mes yeux,
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 jusqu’à ce que, pénétrant dans le sanctuaire de Dieu, je me fusse rendu compte de leur fin.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Oui, tu les as mis sur un chemin glissant, tu les précipites dans la ruine.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 Oh! comme, en un instant, ils sont réduits à la désolation! Ils sont perdus, ils finissent dans l’épouvante.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 Comme un songe s’évanouit après le réveil, ainsi, Seigneur, quand tu te lèves, tu dissipes leurs vaines images.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 Ainsi, quand mon cœur s’aigrissait et que mes reins étaient transpercés,
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 j’étais un sot, ne sachant rien; j’étais comme une brute à ton égard.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Mais désormais je resterai toujours avec toi: tu as saisi ma main droite;
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 tu me guideras par ton conseil, et finalement tu me recueilleras avec honneur.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Qui donc aurais-je sans toi au ciel? A côté de toi, je ne désire rien sur terre.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Ma chair peut se dissoudre ainsi que mon cœur, Dieu sera à jamais le rocher de mon cœur et mon partage.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 Certainement ils périront ceux qui s’éloignent de toi; tu anéantis tous ceux qui te deviennent infidèles.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 Pour moi, le voisinage de Dieu fait mon bonheur; j’ai mis ma confiance dans le Seigneur Dieu, prêt à proclamer toutes tes œuvres.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.