< Psaumes 7 >

1 Chigayon de David, qu’il chanta à l’Eternel à propos de Couchi, le Benjamite. Eternel, mon Dieu, en toi je m’abrite; assiste-moi contre tous mes persécuteurs, délivre-moi.
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 Sans cela, on déchirerait, tel un lion, ma personne, on me mettrait en pièces, et nul ne me sauverait.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 Eternel, mon Dieu, si j’ai agi de la sorte, s’il y a de l’iniquité en mes mains:
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 si j’ai rendu la pareille à qui m’a fait du mal, et dépouillé qui m’a pris en haine sans motif,
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 que l’ennemi se mette à ma poursuite et m’atteigne! qu’il broie ma vie sur le sol, et traîne mon honneur dans la poussière! (Sélah)
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Lève-toi, Seigneur, dans ta colère, oppose-toi à la fureur de mes adversaires, et, en ma faveur, exerce la justice que tu as proclamée.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 Que l’assemblée des peuples se groupe autour de toi! t’élevant au-dessus d’elle, regagne ta sublime résidence.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 Seigneur, qui juges les nations, rends-moi justice, selon ma vertu et ma droiture.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 Que la méchanceté des impies ait donc un terme! Affermis le juste, ô toi qui sondes cœurs et reins, Dieu équitable!
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Ma sauvegarde est en Dieu: il secourt les cœurs droits.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 Dieu est un juge équitable, le Tout-Puissant fait sentir sa colère tous les jours:
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 si l’on ne s’amende pas, il aiguise son glaive, il bande son arc et l’ajuste.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 Il s’arme d’engins meurtriers, de ses flèches il fait des brandons.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Voyez, le méchant ourdit l’iniquité, il conçoit le mal et enfante le mensonge;
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 il a creusé une fosse et l’a rendue profonde, mais il glisse dans le précipice qu’il a préparé.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 Son injustice lui retombe sur la tête, et sur son crâne sa cruauté s’abat.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 Je rendrai grâce à l’Eternel pour sa justice, et je chanterai le nom du Seigneur, du Très-Haut.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psaumes 7 >