< Psaumes 68 >

1 Au chef des chantres. De David. Psaume. Cantique. Que Dieu se lève! Que ses ennemis se dispersent, que ceux qui le haïssent s’enfuient crevant sa face!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 Comme s’évanouit, se dissipe la fumée, comme la cire se fond au feu, ainsi périssent les méchants en présence de Dieu!
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 Mais que les justes se réjouissent, jubilent devant Dieu, et s’abandonnent à des transports de joie!
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Entonnez des chants à Dieu, célébrez son nom, exaltez Celui qui chevauche dans les hauteurs célestes, Eternel est son nom! et faites éclater votre allégresse devant lui.
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 Dans sa sainte résidence, Dieu est le père des orphelins, le défenseur des veuves.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 Dieu donne un foyer à ceux qui vivent solitaires; il rend la liberté avec le bien-être aux prisonniers, mais les rebelles restent confinés dans des régions arides.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 O Dieu, quand tu sortis à la tête de ton peuple, quand tu t’avanças dans les solitudes lugubres, (Sélah)
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 la terre trembla, les cieux aussi se fondirent à la vue de Dieu, ce Sinaï lui-même, à la vue du Dieu d’Israël.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 Tu fis ruisseler, ô Dieu, une pluie bienfaisante; ainsi toi-même tu restauras ton héritage, si épuisé.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Tes légions s’y établirent, dans ce domaine que, dans ta bonté, ô Dieu, tu avais préparé pour ces malheureux.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 Le Seigneur fit entendre sa parole, des messages de bonheur en grande quantité:
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 "Les rois des armées se sont enfuis, enfuis! Et celle qui garde la maison répartit le butin.
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 Resterez-vous immobiles entre les parcs de troupeaux, ô vous, ailes de la colombe, plaquées d’argent, dont les pennes ont la couleur éclatante de l’or fin?
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 Quand le Tout-Puissant dispersa les rois, le Çalmon était couvert de neige."
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 Montagnes de Dieu, montagnes de Basan, montagnes aux croupes élevées, montagnes de Basan!
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 Pourquoi, montagnes aux croupes élevées, pourquoi jalousez-vous la montagne que Dieu a désirée pour sa résidence? Oui, il y demeurera durant toute l’éternité.
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 Les chars de Dieu se comptent par myriades et milliers répétés; avec eux le Seigneur se rend sur le Sinaï, dans le Sanctuaire.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 Tu es remonté dans les hauteurs, après avoir fait des prises; tu as reçu des dons parmi les hommes; même des rebelles sont contraints de demeurer près de l’Eternel, près de Dieu.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Loué soit le Seigneur! Jour par jour il nous accable de ses bienfaits, lui, le Dieu de notre salut. (Sélah)
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Le Tout-Puissant est pour nous un Dieu sauveur, grâce à Dieu, notre Seigneur, on échappe à la mort.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 Mais Dieu fracasse la tête de ses ennemis, le crâne chevelu de quiconque suit une voie criminelle.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 Le Seigneur a dit: "De Basan, je ramènerai mon peuple, je le ramènerai des profondeurs de la mer,
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 pour que ton pied baigne dans le sang, et que la langue de tes chiens ait sa part dans les dépouilles des ennemis."
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 On a vu ta marche triomphale, ô Dieu, la marche de mon Dieu, de mon Roi, en son Sanctuaire.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 En tête sont les chanteurs, puis viennent les joueurs d’instruments, au milieu de jeunes filles battant du tambourin.
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 "Dans vos groupes, Bénissez Dieu! Bénissez le Seigneur, vous tous, issus de la source d’Israël!
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 Là c’est Benjamin, le plus jeune, qui dirige la procession, les princes de Juda s’avancent avec leurs frondeurs, puis les princes de Zabulon, les princes de Nephtali."
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 L’Eternel a décrété ta victoire, c’est un triomphe, ô Dieu, que tu as préparé pour nous.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 De ton sanctuaire, tu veilles sur Jérusalem; à toi les Rois apportent des présents.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Gourmande la bête tapie dans les joncs, la troupe des puissants taureaux mêlés aux bouvillons des nations, qui viennent s’humilier, munies de lingots d’argent. Dieu disperse les peuples qui aiment les batailles.
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 De grands personnages arrivent de l’Egypte; l’Ethiopie tend avidement ses mains vers Dieu.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 O Royaumes de la terre, entonnez des chants à Dieu! Célébrez le Seigneur, (Sélah)
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 Célébrez Celui qui chevauche les cieux antiques; voici qu’il fait retentir sa voix, une voix formidable.
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 Proclamez la puissance de Dieu; sa majesté s’étend sur Israël, et sa force éclate dans les nuées.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 Tu apparais redoutable, ô Dieu, du fond de ton sanctuaire; le Dieu d’Israël octroie force et vigueur au peuple. Que Dieu soit béni!
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< Psaumes 68 >