< Psaumes 53 >
1 Au chef des chantres; sur Mahalat. Maskîl de David. L’Impie a dit en son cœur: "Il n’est point de Dieu!" On est corrompu, on commet des actes odieux; personne ne fait le bien.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat. Wani maskil na Dawuda. Wawa ne kawai yakan ce a zuciyarsa, “Ba Allah.” Sun lalace, kuma hanyoyinsu ba su da kyau; babu wani mai aikata abu mai kyau.
2 Dieu, du haut du ciel, regarde les hommes, pour voir s’il en est de bien inspirés, recherchant Dieu.
Allah yana duba daga sama a kan’ya’yan mutane yă ga ko akwai wani wanda ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 Tous ils ont dévié, ensemble ils sont pervertis; personne n’agit bien, pas même un seul.
Kowa ya kauce, gaba ɗaya sun lalace; babu guda da yake aikata abu mai kyau, babu ko ɗaya.
4 Ah! ils s’en ressentiront, tous ces ouvriers d’iniquité, qui dévorent mon peuple comme on mange du pain, et n’invoquent point Dieu.
Masu aikata mugunta ba sa taɓa koyo? Suna cin mutanena kamar yadda ake cin burodi, ba sa kuma kira ga Allah.
5 Là même ils seront saisis d’effroi, où il n’y a pas lieu de s’effrayer; car Dieu disperse les membres de ceux qui t’assiègent. Tu les couvres de honte, Dieu les ayant rejetés.
Ga shi fa, sun firgita don tsoro, ko da yake babu dalilin tsoro, gama Allah zai watsar da ƙasusuwan masu ƙinsa, za su sha kunya, gama Allah ya ƙi su.
6 Ah! puisse venir de Sion le salut d’Israël! Quand Dieu ramènera les captifs de son peuple, Jacob jubilera, Israël sera dans la joie.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Allah ya sāke arzuta mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!