< Psaumes 31 >

1 Au chef des chantres. Psaume de David. En toi, Seigneur, je m’abrite! Puissé-je n’être jamais déçu! Dans ta justice, retire-moi du danger.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
2 Incline vers moi ton oreille, délivre-moi promptement, sois pour moi un rocher tutélaire, une forte citadelle qui puisse me protéger.
Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
3 Car tu es bien mon rocher et ma citadelle, et pour l’amour de ton nom tu me guides et me diriges.
Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
4 Tu me dégageras du filet qu’on m’a dressé, puisque tu es ma sauvegarde.
Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
5 En ta main je confie mon esprit, tu me délivres, Eternel, Dieu de vérité.
Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
6 Je hais ceux qui s’attachent à de vaines idoles; pour moi, je mets ma confiance en l’Eternel.
Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
7 Je serai heureux et en joie par ta bonté, puisque tu as vu ma misère, reconnu les tourments de mon âme.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
8 Tu ne m’as pas livré au pouvoir de l’ennemi; tu as mis mes pieds au large.
Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
9 Sois-moi propice, ô Seigneur! Car je me trouve en détresse. Par le chagrin ma vue s’est usée, ainsi que mon âme et mon corps.
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
10 En effet, ma vie s’écoule dans la peine, mes années dans les gémissements; ma vigueur est tombée à cause de mon iniquité, mes membres sont à bout de forces.
Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
11 A cause de tous mes ennemis, je suis un objet d’opprobre, de grand opprobre pour mes voisins, une cause de terreur pour mes intimes. Ceux qui me voient dans la rue s’écartent de moi.
Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
12 Mon souvenir disparaît des cœurs comme celui d’un mort, je suis tel qu’un vase perdu.
An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
13 Oui, j’entends les mauvais propos de la foule, répandant la terreur à l’entour, quand on se ligue ensemble contre moi, complotant de m’enlever la vie.
Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
14 Moi, cependant, j’ai confiance en toi, Seigneur, je dis: "Tu es mon Dieu!"
Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
15 Mes destinées sont dans ta main: délivre-moi de mes ennemis et persécuteurs.
Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
16 Fais luire ta face sur ton serviteur, secours-moi par ta grâce.
Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
17 Seigneur! que je ne sois point déçu quand je t’invoque! que les méchants, eux, soient confondus et réduits au silence du Cheol! (Sheol h7585)
Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
18 Qu’elles deviennent muettes, les lèvres menteuses, qui parlent avec insolence contre le juste, par excès d’orgueil et de mépris!
Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
19 Ah! qu’elle est grande ta bonté, que tu tiens en réserve pour tes adorateurs, que tu témoignes à ceux qui ont foi en toi, en face des fils de l’homme!
Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
20 Tu les protèges, à l’abri de ta face, contre les intrigues des gens, tu les mets à couvert, dans ta tente, contre la guerre des langues.
Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
21 Loué soit le Seigneur, car il a fait éclater sa bonté pour moi, en une ville fortifiée!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
22 Et je disais, moi, dans mon trouble: "Je suis banni loin de tes yeux! Mais tu as entendu ma voix suppliante, lorsque je t’implorais.
Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
23 Aimez l’Eternel, vous tous, ses pieux adorateurs! Le Seigneur veille sur ceux qui sont fidèles, mais il paie avec usure quiconque agit avec orgueil.
Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
24 Soyez forts, ayez le cœur ferme, vous tous qui espérez en l’Eternel!
Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.

< Psaumes 31 >