< Psaumes 22 >

1 Au chef des chantres. D’Après l’Ayyélet Hachahar. Psaume de David. Mon Dieu, mon Dieu, pourquoi m’as-tu abandonné, loin de me porter secours, d’entendre mes paroles suppliantes?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Mon Dieu, j’appelle de jour et tu ne réponds pas, de nuit, et il n’est pas de trêve pour moi.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Tu es pourtant le Saint, trônant au milieu des louanges d’Israël.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 En toi nos pères ont eu confiance, ils ont eu confiance, et tu les as sauvés.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Ils ont crié vers toi et ont été délivrés; ils ont espéré en toi et n’ont pas été déçus.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Moi, je suis un vermisseau, et non un homme, l’opprobre des gens, objet de mépris pour le peuple.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Tous ceux qui me voient se moquent de moi, grimacent des lèvres, hochent la tête.
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 "Qu’il s’en remette à l’Eternel! Que celui-ci le sauve, qu’il l’arrache du danger, puisqu’il l’aime!"
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Oui, c’est toi qui m’as tiré des entrailles maternelles, qui m’as fait reposer en sûreté dans le giron de ma mère;
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 entre tes bras j’ai été jeté dès ma naissance, dès le sein de ma mère, tu as été mon Dieu.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Ne t’éloigne pas de moi car l’angoisse est proche, et nul n’est là pour m’aider.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Des taureaux nombreux m’environnent, des bêtes puissantes de Basan m’assiègent.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Ils ouvrent contre moi leur gueule, tel un lion qui déchire et qui rugit.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Je suis comme l’eau qu’on répand, tous mes membres se disloquent; mon cœur est comme de la cire, qui fondrait au milieu de mes entrailles.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Ma sève est desséchée comme un tesson, ma langue est collée à mon palais; tu m’étends dans la poussière de la mort.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Car des chiens m’enveloppent, la bande des méchants fait cercle autour de moi; comme le lion ils meurtrissent mes mains et mes pieds.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Je pourrais compter tous mes os; eux, ils me toisent et se repaissent de ma vue.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Ils se partagent mes habits, ils tirent au sort mes vêtements.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Mais toi, ô Seigneur, ne t’éloigne pas; toi, qui es ma force, viens vite à mon secours!
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Sauve mon âme du glaive, ma vie de la fureur des chiens;
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 arrache-moi de la gueule du lion, protège-moi contre les cornes des buffles.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Je proclamerai ton nom devant mes frères, au milieu de l’assemblée, je te louerai.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 "Adorateurs de l’Eternel, louez-le vous tous, descendants de Jacob, honorez-le; révérez-le, vous tous, postérité d’Israël!
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Car il n’a point dédaigné, il n’a point méprisé la misère du malheureux; il n’a pas caché de lui son visage, ni manqué de l’entendre quand il implorait!"
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 C’Est toi dont je célébrerai les louanges dans la grande assemblée, j’accomplirai mes vœux devant ceux qui te craignent.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Les humbles mangeront et seront rassasiés, les adorateurs de l’Eternel le loueront. Que votre cœur renaisse à la vie pour toujours!
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Les confins de la terre se souviendront et reviendront au Seigneur, toutes les familles des peuples se prosterneront devant lui.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Car à l’Eternel appartient la royauté, il domine sur toutes les nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Ils mangeront et adoreront, tous les heureux de la terre; devant lui s’inclineront ceux qui descendent dans la poussière, incapables de sustenter leur vie.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 La postérité lui vouera un culte; on parlera du Seigneur aux âges à venir.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 IIs viendront et proclameront sa justice: ils diront au peuple à naître ce qu’il a fait.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Psaumes 22 >