< Psaumes 105 >

1 Rendez hommage à l’Eternel, proclamez son nom, publiez parmi les nations ses hauts faits.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Chantez en son honneur, célébrez-le, entretenez-vous de toutes ses merveilles.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Glorifiez-vous de son saint nom; que le cœur de ceux qui recherchent l’Eternel soit en joie!
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Mettez-vous en quête de l’Eternel et de sa puissance, aspirez constamment à jouir de sa présence.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Souvenez-vous des merveilles qu’il a opérées, de ses prodiges et des arrêts sortis de sa bouche,
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 vous, ô postérité d’Abraham, son serviteur, fils de Jacob, ses élus!
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Il est, lui, l’Eternel, notre Dieu; ses jugements s’étendent à toute la terre.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Eternellement il garde le souvenir de son alliance, du pacte qu’il a promulgué pour mille générations,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 qu’il a conclu avec Abraham, qu’il a fait par serment avec Isaac.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 Il l’a érigé en loi pour Jacob, en contrat immuable pour Israël.
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 "C’Est à toi, disait-il, que je donnerai le pays de Canaan comme un lot héréditaire",
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 alors qu’ils étaient encore en petit nombre, et à peine établis comme étrangers dans ce pays.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 Puis ils se mirent à errer de nation en nation, d’un royaume vers un autre peuple.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Il ne permit à personne de les opprimer, et à cause d’eux il châtia des rois.
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 "Ne touchez pas à mes oints, ne faites pas de mal à mes prophètes!"
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Il appela la famine sur la terre, et anéantit toute ressource en pain.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Mais déjà il avait envoyé devant eux un homme: Joseph avait été vendu comme esclave.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 On chargea ses pieds de liens, son corps fut retenu par les fers,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 jusqu’à ce que s’accomplit sa prédiction et que la parole du Seigneur l’eût innocenté.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Le roi donna ordre d’ouvrir sa prison, le souverain des peuples, de faire tomber ses chaînes.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Il l’établit chef de sa maison, intendant de tous ses biens,
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 avec la mission d’enchaîner les seigneurs à sa volonté, d’apprendre la sagesse aux vieux conseillers.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Puis Israël vint en Egypte, Jacob alla séjourner dans le pays de Cham,
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 et Dieu multiplia prodigieusement son peuple, le rendit plus nombreux que ses oppresseurs.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Leur cœur changea jusqu’à prendre son peuple en haine, et ourdir des machinations contre ses serviteurs.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Il délégua Moïse, son serviteur, Aaron qu’il avait élu.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Ils accomplirent parmi eux les miracles qu’il avait annoncés, ses prodiges dans le pays de Cham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Il répandit des ténèbres qu’il rendit impénétrables, pour qu’ils ne résistassent pas à sa parole.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Il changea leurs eaux en sang, et fit périr leur poisson.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Leur pays fut inondé de grenouilles, jusque dans les appartements de leurs rois.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Il dit, et des bêtes malfaisantes firent irruption, la vermine sévit dans toute leur contrée.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 En guise de pluie, il leur envoya de la grêle, du feu, des flammes dans leur pays.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Il dévasta leurs vignes et leurs figuiers, et fracassa les arbres de leur territoire.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Il dit, et des sauterelles vinrent, des locustes en nombre infini,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 qui dévorèrent toutes les plantes de leurs champs et dévorèrent les fruits de leur sol.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Puis il frappa tout premier-né dans leur pays, les prémices de toute leur vigueur.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Il les fit sortir, chargés d’argent et d’or; nul parmi ses tribus ne faiblit.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Les Egyptiens se réjouirent de leur départ, car ils avaient été saisis d’épouvante à cause d’eux.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Il déploya une nuée comme un voile protecteur, un feu pour éclairer la nuit.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Ils réclamèrent, et il amena des cailles, les nourrit à satiété d’un pain du ciel.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Il fendit la roche et des eaux jaillirent, s’épandant dans les régions arides comme un fleuve.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 C’Est qu’il se souvint de sa sainte promesse à Abraham, son serviteur;
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 il fit donc sortir son peuple dans l’allégresse, ses élus avec des chants joyeux.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 Il leur octroya des terres occupées par des peuples: ils héritèrent du labeur d’autres nations,
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 afin qu’ils observassent ses statuts et respectassent ses lois. Alléluia!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psaumes 105 >