< Proverbes 31 >
1 Paroles du roi Lemouel. Leçon solennelle que lui inculqua sa mère.
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2 "Ah! mon fils! Ah! enfant de mes entrailles! Ah! fils que j’ai appelé de mes vœux!
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3 Ne prodigue paso ta vigueur aux femmes, ne livre pas tes destinées à celles qui perdent les rois.
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4 Ce n’est pas aux rois, ô Lemouel, ce n’est pas aux rois qu’il sied de boire du vin, ni aux princes de s’adonner aux liqueurs fortes;
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5 de peur qu’en buvant, ils n’oublient les lois et ne méconnaissent le droit de toutes les victimes de la misère.
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6 Donnez des liqueurs fortes aux malheureux, du vin à ceux qui ont l’amertume au cœur.
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7 Qu’ils boivent, et qu’ils oublient leur misère; qu’ils perdent le souvenir de leur chagrin!
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8 Ouvre la bouche en faveur du muet, pour la défense de tous les vaincus du sort.
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9 Ouvre la bouche pour juger avec équité et faire droit au pauvre et à l’indigent.
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10 Heureux qui a rencontré une femme vaillante! Elle est infiniment plus précieuse que les perles.
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11 En elle le cœur de son époux a toute confiance; aussi les ressources ne lui font-elles pas défaut.
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12 Tous les jours de sa vie, elle travaille à son bonheur: jamais elle ne lui cause de peine.
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13 Elle se procure de la laine et du lin et accomplit sa besogne d’une main diligente.
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 Pareille aux vaisseaux marchands, elle amène de loin ses provisions.
Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15 Il fait encore nuit qu’elle est déjà debout, distribuant des vivres à sa maison, des rations à ses servantes.
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16 Elle jette son dévolu sur un champ et l’acquiert; avec le produit de son travail elle plante un vignoble.
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17 Elle ceint de force ses reins et arme ses bras de vigueur.
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18 Elle s’assure que ses affaires sont prospères; sa lampe ne s’éteint pas la nuit.
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19 Ses mains saisissent le rouet, ses doigts manient le fuseau.
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20 Elle ouvre sa main au pauvre et tend le bras au nécessiteux.
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21 Elle ne redoute point la neige pour sa maison, car tous ses gens sont couverts de riches étoffes.
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22 Elle se brode des tapis. Lin fin et pourpre forment ses vêtements.
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 Son époux est considéré aux Portes, quand il siège avec les anciens du pays.
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24 Elle confectionne des tissus, qu’elle vend, et des ceintures, qu’elle cède au marchand.
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
25 Parée de force et de dignité, elle pense en souriant à l’avenir.
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26 Elle ouvre la bouche avec sagesse, et des leçons empreintes de bonté sont sur ses lèvres.
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27 Elle dirige avec vigilance la marche de sa maison, et jamais ne mange le pain de l’oisiveté.
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28 Ses fils se lèvent pour la proclamer heureuse, son époux pour faire son éloge:
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29 "Bien des femmes se sont montrées vaillantestu leur es supérieure à toutes!"
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 Mensonge que la grâce! Vanité que la beauté! La femme qui craint l’Eternel est seule digne de louanges.
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31 Rendez-lui hommage pour le fruit de ses mains, et qu’aux Portes ses œuvres disent son éloge!
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.