< Néhémie 9 >

1 Le vingt-quatrième jour du même mois, les enfants d’Israël s’assemblèrent pour un jeûne, revêtus de cilices et couverts de terre.
A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, Isra’ilawa suka taru, suna yin azumi, suna sa rigunan makoki, suna kuma zuba toka a kansu.
2 Ceux de la race d’Israël se séparèrent de tous les fils de l’étranger; ils se présentèrent et confessèrent leurs péchés et les fautes de leurs pères.
Waɗanda suke zuriyar Isra’ilawa suka ware kansu daga dukan baƙi. Suka tsaya, suka kuma furta zunubansu da muguntar kakanninsu.
3 Se tenant à la même place, ils lurent pendant un quart de la journée dans le livre de la loi de l’Eternel, leur Dieu, et pendant un autre quart ils se confessèrent et se prosternèrent devant l’Eternel, leur Dieu.
Sa’ad da suke nan a tsaye, aka ɗauki awa uku ana karanta Littafin Dokar Ubangiji Allahnsu. Aka kuma ɗauki awa uku ana sujada ga Ubangiji Allahnsu.
4 Sur la tribune des Lévites prirent place Yêchoua, Bâni, Kadmiêl, Chebania, Bounni, Chèrèbia, Bâni, Kenani, et ils implorèrent à pleine voix l’Eternel, leur Dieu.
A kan dakalin kuwa akwai Lawiyawa, wato, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani da Kenani tsaye, waɗanda suka kira da babbar murya ga Ubangiji Allahnsu.
5 Les Lévites Yêchoua, Kadmiêl, Bâni, Hachabneya, Chèrèbia, Hodia, Chebania, Petahia dirent: "Levez-vous, bénissez l’Eternel, votre Dieu, qui existe d’éternité en éternité! Oui, qu’on bénisse ton nom glorieux, qui est élevé au-dessus de toute bénédiction et de toute louange!
Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.
6 C’Est toi seul qui es l’Eternel; c’est toi qui as fait les cieux et les cieux des cieux avec toutes leurs milices, la terre et tout ce qui la couvre, les mers et tout ce qu’elles renferment: tu donnes la vie à tous les êtres, et l’armée du ciel s’incline devant toi.
Kai kaɗai ne Ubangiji. Kai ka yi sammai, har ma da sama sammai, da dukan rundunar taurari, da duniya da kuma dukan abin da yake cikinta, da tekuna da dukan abubuwan da suke cikinsu. Ka ba da rai ga kome, kuma rundunonin sama suna maka sujada.
7 C’Est toi, Eternel, Dieu, qui élus Abram, qui le fis sortir d’Our-Kasdîm et le dénommas Abraham.
“Kai ne Ubangiji Allah, wanda ya zaɓi Abram, ya fitar da shi daga Ur na Kaldiyawa, ya kuma ba shi suna Ibrahim.
8 Tu trouvas son cœur fidèle à ton égard et tu lui fis la promesse solennelle de donner le pays du Cananéen, du Héthéen, de l’Amorréen, du Phérézéen, du Jébuséen, du Ghirgachéen de le donner à sa postérité, et tu as accompli tes paroles, car tu es juste.
Kai ka sami zuciyarsa da aminci a gare ka, ka kuma yi alkawari da shi cewa za ka ba zuriyarsa ƙasar Kan’aniyawa, da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, da ta Yebusiyawa, da kuma ta Girgashiyawa. Ka kiyaye alkawarinka domin kai mai adalci ne.
9 Tu vis la misère de nos pères en Egypte, et leurs cris, tu les entendis près de la mer des joncs.
“Ka ga wahalar kakanninmu a Masar; ka kuwa ji kukansu a Jan Teku.
10 Tu opéras des signes et des prodiges sur Pharaon, sur tous ses serviteurs et tout le peuple de son pays, car tu avais reconnu qu’on avait agi tyranniquement à leur égard. Ainsi tu t’es fait un renom qui s’est maintenu jusqu’à ce jour.
Ka aika da alamu masu banmamaki da al’ajabai a kan Fir’auna, a kan dukan shugabanninsa da kuma a kan dukan mutanen ƙasarsa, gama ka ga irin danniyar da suka yi wa mutanenka. Ka samo wa kanka suna, wadda ta dawwama har yă zuwa yau.
11 Tu fendis la mer devant eux; ils passèrent à pied sec au milieu de la mer, tandis que leurs persécuteurs, tu les précipitas au fond du gouffre, comme une pierre au sein des eaux puissantes.
Ka raba teku a gaban kakanninmu, saboda su wuce cikinsa a busasshiyar ƙasa, amma ka hallaka masu binsu cikin zurfafa, nutse kamar dutse a cikin ruwa.
12 Tu les guidas, le jour, par une colonne de nuée et, la nuit, par une colonne de feu, destinée à éclairer devant eux la route qu’ils devaient suivre.
Da rana ka bishe kakanninmu da girgije, da dare kuwa ka bishe su da ginshiƙin wuta don ka ba su haske a hanyar da za su bi.
13 Tu descendis sur la montagne de Sinaï, et tu leur parlas du haut du ciel tu leur donnas des statuts équitables, des doctrines de vérité, des ordonnances et des préceptes excellents.
“Ka sauko a kan Dutsen Sinai; ka yi musu magana daga sama. Ka ba su ƙa’idodi da dokokin da suke masu adalci da kuma daidai, ka ba su farillai da umarnai da suke da kyau.
14 Tu leur fis connaître ton sabbat saint et, par l’organe de Moïse, ton serviteur, tu leur prescrivis des commandements, des lois et une doctrine.
Ka sanar da su Asabbacinka mai tsarki, ka kuma ba su umarnai, da farillai, da kuma dokoki ta wurin bawanka Musa.
15 Du haut du ciel tu leur octroyas du pain pour leur faim, tu leur fis jaillir de l’eau du rocher pour leur soif, et tu leur dis de marcher à la conquête du pays que tu avais promis solennellement de leur donner.
Cikin yunwansu ka ba su burodi daga sama, cikin ƙishirwansu kuma ka fitar musu ruwa daga dutse. Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka rantse ta wurin ɗaga hannu cewa za ka ba su.
16 Mais eux, nos ancêtres, agirent avec témérité, ils raidirent leur cou et refusèrent d’obéir à tes ordres.
“Amma su kakanninmu, suka yi fariya da taurinkai, ba su kuwa yi biyayya ga umarnanka ba.
17 Oui, ils refusèrent d’obéir, oublieux de tes merveilles, que tu avais opérées en leur faveur; ils raidirent leur cou et, dans leur rébellion, se donnèrent un chef pour retourner dans leur servitude. Mais toi, tu es un Dieu de pardon, clément, miséricordieux, tardif à la colère et abondant en grâce: tu ne les as pas abandonnés.
Suka ƙi su saurare ka, suka kāsa tuna da mu’ujizan da ka aikata a cikinsu. Suka yi taurinkai, cikin tawayensu kuma suka naɗa shugaba don su koma bautarsu. Amma kai Allah ne mai gafartawa, mai alheri da jinƙai, mai jinkirin fushi, mai yalwar ƙauna. Saboda haka ba ka yashe su ba,
18 Bien plus, ils se firent un veau de métal et dirent: "Voilà ton Dieu qui t’a fait sortir de l’Egypte," commettant ainsi de grands blasphèmes.
ko ma sa’ad da suka yi wa kansu siffar ɗan maraƙi, suka ce, ‘Wannan shi ne allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar,’ ko sa’ad da suka yi saɓo mai bantsoro.
19 Cependant toi, dans ton immense miséricorde, tu ne les délaissas point dans le désert: la colonne de nuée, ne s’écartant pas d’eux le jour, continuait à les guider sur la route, de même que, de nuit, la colonne de feu éclairait pour eux le chemin qu’ils devaient suivre.
“Saboda jinƙanka mai girma, ba ka yashe su a hamada ba. Da rana, ginshiƙin girgije bai daina bishe su a hanyarsu ba, da dare kuma ginshiƙin wuta bai daina haskakawa a hanyar da za su bi ba.
20 Tu les favorisas de ton esprit de bienveillance pour les instruire, tu ne refusas pas ta manne à leur bouche et tu leur donnas de l’eau pour leur soif.
Ka ba da Ruhunka mai kyau don yă koyar da su. Ba ka janye Manna naka daga bakunansu ba, ka kuma ba su ruwa don ƙishirwansu.
21 Pendant quarante ans, tu les entretins dans le désert, sans qu’ils manquassent de rien; leurs vêtements ne s’usèrent pas ni leurs pieds ne furent meurtris.
Shekaru arba’in ka riƙe su a cikin hamada; ba su rasa kome ba, rigunansu ba su yage ba, ƙafafunsu kuwa ba su kumbura ba.
22 Tu leur livras des royaumes et des peuples, que tu leur répartis dans toute direction, et ils prirent possession du pays de Sihôn, du pays du roi de Hesbôn et du pays d’Og, roi de Basan.
“Ka ba su mulkoki da al’ummai, kana ba su har ma da ƙasashen da suke jeji. Suka ci ƙasar Sihon na sarkin Heshbon da ƙasar Og inda sarkin Bashan yake mulki.
23 Tu multiplias leurs enfants comme les étoiles du ciel, et tu les amenas dans le pays que tu avais dit à leurs pères d’aller conquérir.
Ka sa’ya’yansu maza suka yi yawa kamar taurarin sararin sama, ka kuma kawo su cikin ƙasar da ka faɗa wa kakanninsu su shiga su mallake.
24 Et les enfants vinrent prendre possession de ce pays; tu fis plier devant eux les habitants du pays, les Cananéens, et tu livras entre leurs mains tant les rois que les peuples de ce pays, pour agir envers eux selon leur volonté.
’Ya’yansu maza suka shiga suka kuma mallaki ƙasar. A gabansu ka rinjayi Kan’aniyawan da suke zama a cikin ƙasar; ka ba da Kan’aniyawa a gare su, tare da sarakunansu da kuma mutanen ƙasar, su yi da su yadda suke so.
25 Ils s’emparèrent de villes fortes et d’un territoire fertile, ils prirent possession de maisons abondantes en biens, de citernes toutes creusées, de vignobles, d’oliviers et d’arbres fruitiers en quantité; ils en mangèrent, s’en rassasièrent, devinrent gras et vécurent dans les délices par ta grande bonté.
Suka kame birane masu katanga masu ƙarfi, da ƙasa masu ba da amfani; suka mallaki gidaje cike da kowane irin abu mai kyau, da rijiyoyin da aka riga aka haƙa, da gonakin inabi, da gonakin itatuwan zaitun da kuma itatuwan ba da’ya’ya a yalwace a ciki. Suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba; suka ji daɗi cikin alherinka mai girma.
26 Mais alors ils devinrent rebelles et s’insurgèrent contre toi; ils tournèrent le dos à ta loi, mirent à mort tes prophètes, qui leur faisaient la leçon pour les ramener à toi, et se rendirent coupables de grands blasphèmes.
“Amma suka yi rashin biyayya suka kuma yi tawaye gare ka; suka sa dokarka a bayansu. Suka kashe annabawanka waɗanda suka gargaɗe su don su mai da su gare ka; suka aikata saɓo mai bantsoro.
27 Et tu les abandonnas aux mains de leurs adversaires, qui les opprimèrent. Au temps de leur détresse ils criaient vers toi, et toi, du haut du ciel, tu les exauçais et, grâce à ton extrême miséricorde, tu leur donnais des sauveurs pour les délivrer du pouvoir de leurs ennemis.
Saboda haka ka miƙa su ga abokan gābansu waɗanda suka yi musu danniya. Amma sa’ad da ake danniyarsu sai suka yi kuka gare ka. Daga sama ka ji su, cikin jinƙanka mai girma kuwa ka ba su mai ceto, wanda ya fisshe su daga hannun abokan gābansu.
28 Mais dès qu’ils avaient retrouvé du repos, ils recommençaient à faire le mal devant toi, et toi, de les abandonner aux mains de leurs ennemis, qui les opprimaient. Puis, de nouveau, ils t’imploraient et toi, du haut du ciel, tu les entendais et les délivrais, grâce à ta miséricorde, maintes et maintes fois.
“Amma nan da nan, da suka sami hutu, sai suka sāke aikata abin da yake mugu a idonka. Sai ka yashe su ga hannun abokan gābansu don su yi mulki a kansu. Sa’ad da suka yi kuka kuma gare ka, ka ji daga sama, cikin jinƙanka kuma ka fisshe su sau da sau.
29 Tu leur faisais des remontrances pour les ramener à ta loi; mais eux, ils étaient arrogants, n’obéissant pas à tes préceptes et péchant contre tes statuts, par lesquels l’homme, qui les pratique, obtient la vie; ils présentaient un cou rebelle, raidissaient leur nuque et n’écoutaient point.
“Ka gargaɗe su su dawo ga dokarka, amma suka yi fariya, suka bijire wa umarnanka. Suka yi zunubi game da farillanka waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu in ya yi biyayya da su. Cikin taurinkai suka juye bayansu daga gare ka, suka zama masu taurinkai, suka kuma ƙi su saurara.
30 Tu patientas ainsi à leur égard de longues années; avec le concours de tes prophètes, tu les admonestas par ton inspiration, mais ils ne prêtèrent point l’oreille; aussi les livras-tu aux mains des nations des autres pays.
Shekaru masu yawa ka yi haƙuri da su. Ta wurin Ruhunka ka gargaɗe su ta wurin annabawa. Duk da haka ba su kasa kunne ba, saboda haka ka miƙa su ga maƙwabtansu.
31 Cependant, dans ta grande miséricorde, tu ne les as pas complètement anéantis ni délaissés, car tu es un Dieu clément et miséricordieux.
Amma cikin tausayinka mai girma ba ka kawo su ga ƙarshe ko ka yashe su ba, gama kai Allah ne mai alheri da kuma mai jinƙai.
32 Et maintenant, notre Dieu, ô Dieu grand, puissant et redoutable, qui gardes fidèlement le pacte de bienveillance, ne fais pas trop peu de cas de toutes les tribulations que nous avons éprouvées, nous, nos rois, nos princes, nos prêtres, nos prophètes, nos ancêtres, ton peuple tout entier depuis l’époque des rois d’Assyrie jusqu’à ce jour.
“To yanzu, ya Allahnmu, mai girma, mai iko, da kuma mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna, kada ka bar dukan wannan wahala ta zama kamar marar muhimmanci a idanunka, wahalar da ta zo a kanmu, a kan sarakunanmu da shugabanni, a kan firistocinmu da annabawa, a kan kakanninmu da kuma dukan mutanenka, daga kwanakin sarakunan Assuriya har yă zuwa yau.
33 Toi, certes, tu as été équitable en tout ce qui nous est advenu; car tu as agi avec loyauté, tandis que nous, nous avons été coupables.
Cikin dukan abubuwan da suka faru da mu, ka kasance mai adalci; ka yi aminci, yayinda mu kuwa muka aikata mugu.
34 Nos rois, nos princes, nos prêtres, nos ancêtres n’ont pas pratiqué ta loi; ils n’ont pas prêté leur attention à tes préceptes ni aux remontrances que tu leur adressais.
Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu da kuma kakanninmu ba su bi dokarka ba, ba su ma mai da hankali ga umarnanka ko gargaɗin da ka yi musu ba.
35 Alors qu’ils étaient dans leur royaume, en possession des biens abondants dont tu les avais gratifiés, du vaste et fertile territoire que tu leur avais assigné, ils ne t’ont pas adoré, ils n’ont pas renoncé à leurs œuvres mauvaises.
Ko ma yayinda suke a masarautarsu, suna jin daɗin girmar kyautatawarka gare su, cikin ƙasar mai girma, da kuma mai fāɗin da ka ba su, ba su bauta maka ko su juye daga mugayen hanyoyinsu ba.
36 Eh bien! Nous voilà aujourd’hui esclaves; oui, dans le pays que tu avais donné à nos pères pour jouir de ses fruits et de ses richesses nous sommes des esclaves!
“Amma duba, mu bayi ne a yau, bayi a ƙasar da ka ba kakanninmu don su ci amfaninta da kuma waɗansu abubuwa masu kyau da take bayarwa.
37 Ses produits, il les prodigue au profit des rois que tu as mis à notre tête à cause de nos péchés; ils dominent sur nos personnes et sur nos troupeaux selon leur gré, et nous, sommes dans une grande détresse!"
Saboda zunubanmu, yalwar girbin da muke samu yana tafiya wurin sarakunan da ka sa a kanmu. Suna mulki bisa jikunanmu, da bisa garkenmu yadda suka ga dama. Muna cikin baƙin ciki.
38 A la suite de tout cela, nous conclûmes un pacte que nous mimes par écrit, et qui fut signé par nos chefs, nos Lévites et nos prêtres.
“Saboda wannan duka, muna yin zaunannen alkawari, muna sa shi a rubuce, shugabanninmu kuwa da Lawiyawanmu, da firistocinmu suna buga hatimansu a kai.”

< Néhémie 9 >