< Michée 7 >

1 Quelle douleur pour moi! Je suis là comme après la récolte des fruits, comme au grappillage qui suit la vendange: pas une grappe à manger, pas une figue tendre pouvant plaire à mon goût!
Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
2 Tout homme de bien a disparu de ce pays, il n’est plus de gens intègres. Tous, ils s’embusquent pour verser le sang, ils se prennent l’un l’autre au piège.
An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
3 Pour favoriser celui qui met la main aux mauvaises besognes, le chef demande, le juge se fait payer, le grand dit hautement ce que convoite son âme, et ainsi on ourdit les intrigues.
Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
4 Le meilleur d’entre eux est comme un amas d’orties, le plus honnête est pire qu’une haie d’épines. Au jour annoncé par tes voyants, ton châtiment surviendra, alors leur désarroi sera au complet.
Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
5 N’Accordez aucune créance à un ami, aucune confiance à un compagnon! Garde ta bouche close devant la femme qui repose sur ton sein.
Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
6 Car le fils vilipende son père, la fille s’insurge contre sa mère, la bru contre sa belle-mère; chacun a pour ennemis les gens de sa maison.
Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
7 Mais moi, je mets mon attente dans le Seigneur, mon espoir dans le Dieu qui assure mon salut, mon Dieu m’entendra.
Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
8 N’Exulte pas à mon sujet, ô mon ennemie, car si je suis tombée, je me relève; si je suis confinée dans les ténèbres, l’Eternel est une lumière pour moi.
Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
9 Je supporterai le courroux de l’Eternel car j’ai péché contre lui jusqu’à ce qu’il prenne ma cause en mains et assure mon bon droit; alors il me ramènera à la lumière, je verrai son œuvre de justice.
Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
10 Mon ennemie en sera témoin et sera couverte de honte, elle qui me dit: "Où est l’Eternel, ton Dieu?" Mes yeux se repaîtront de sa vue; déjà je la vois foulée aux pieds comme la boue des rues.
Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
11 Il viendra un jour où l’on rebâtira tes murs; ce jour-là, tes limites seront reculées.
Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
12 En ce jour, on viendra à toi, depuis l’Assyrie jusqu’aux villes de l’Egypte, et depuis l’Egypte jusqu’au fleuve, d’une mer à l’autre mer et d’une montagne à l’autre.
A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
13 Mais la terre offrira un spectacle de désolation à ses habitants: ce sera le fruit de leurs œuvres.
Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
14 Conduis, avec ta houlette, le troupeau qui est ton héritage: qu’il occupe, solitaire, une forêt dans une région fertile; qu’il pâture en Basan et en Galaad, comme aux jours antiques!
Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
15 Oui, comme à l’époque de ta sortie d’Egypte, je te ferai voir des prodiges.
“Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
16 Les nations en seront témoins et elles auront honte en dépit de toute leur puissance; elles poseront la main sur leur bouche, leurs oreilles seront frappées de surdité.
Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
17 Elles lècheront la poussière comme le serpent, comme les reptiles du sol; elles trembleront au fond de leurs donjons. Craintives, elles accourront vers l’Eternel notre Dieu, et de toi elles auront peur!
Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
18 Quel dieu t’égale Seigneur, toi qui pardonnes les iniquités, qui fais grâce aux offenses, commises par les débris de ton héritage? Toi qui ne gardes pas à jamais ta colère, parce que tu te complais dans la bienveillance?
Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
19 Oui, tu nous reprendras en pitié, tu étoufferas nos iniquités, tu plongeras tous nos péchés dans les profondeurs de la mer.
Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
20 Tu témoigneras à Jacob la fidélité, à Abraham la bienveillance, que tu as jurées à nos pères dès les premiers âges.
Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.

< Michée 7 >