< Malachie 3 >

1 Voici, je vais envoyer mon mandataire, pour qu’il déblaie la route devant moi. Soudain, il entrera dans son sanctuaire, le Maître dont vous souhaitez la venue, le messager de l’alliance que vous appelez de vos vœux: le voici qui vient, dit l’Eternel-Cebaot.
“Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 Mais qui est de force à supporter le jour de son arrivée, à demeurer ferme quand d fera son apparition? Car il est comme le feu du fondeur, comme la potasse des blanchisseurs.
Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
3 Il se mettra à fondre, à épurer de l’argent: il purifiera les fils de Lévi et les affinera comme l’or et l’argent, afin qu’attachés au service de l’Eternel, ils présentent des offrandes avec piété.
Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
4 Alors l’Eternel prendra plaisir aux offrandes de Juda et de Jérusalem, comme il faisait aux jours antiques, dans les années d’autrefois.
Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
5 Et je m’approcherai de vous pour faire justice; je serai un témoin empressé contre les magiciens, contre les adultères, contre les parjures; contre ceux qui font tort au journalier dans son salaire, à la veuve et à l’orphelin, contre les oppresseurs de l’étranger, qui ne s’inquiètent pas de moi, dit l’Eternel-Cebaot.
“Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
6 Parce que moi, Eternel, je ne change pas, vous aussi, enfants de Jacob, n’avez pas été anéantis.
“Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
7 Dès le temps de vos ancêtres, vous avez dévié de mes lois et n’en avez tenu compte. "Revenez à moi, et je reviendrai à vous," dit l’Eternel-Cebaot, et vous dites: "Sur quoi devons-nous revenir?"
Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
8 L’Homme peut-il frauder Dieu? Et cependant vous me fraudez; puis vous dites: "Sur quoi t’avons-nous fraudé?" Sur la dîme et sur les taxes de prélèvement.
“Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
9 La malédiction vous poursuit et c’est moi que vous prétendez frustrer, vous, le peuple tout entier!
Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
10 Apportez toutes les dîmes dans le lieu du dépôt, pour qu’il y ait des provisions dans ma maison, et attendez-moi à cette épreuve, dit l’Eternel-Cebaot: vous verrez si je n’ouvre pas en votre faveur les cataractes du ciel, si je ne répands pas sur vous la bénédiction au-delà de toute mesure.
Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 Et je réprimerai à votre intention le fléau dévastateur, pour qu’il ne détruise plus les fruits de votre sol; et la vigne, dans vos champs, ne sera plus stérile, dit l’Eternel-Cebaot.
Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 Et tous les peuples vous féliciteront, car vous serez, vous, une terre de délices, dit l’Eternel-Cebaot.
“Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
13 Vos paroles ont été violentes contre moi, dit le Seigneur; mais vous dites: "En quoi avons-nous parlé contre toi?"
“Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
14 Vous avez parlé ainsi: "C’Est une chose vaine de servir Dieu; que gagnons-nous à observer son culte et à cheminer tristement dans la crainte de l’Eternel-Cebaot?
“Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
15 Et à présent, nous estimons heureux les impies: vraiment ils sont solidement établis, ceux qui font le mal; oui, ils ont tenté Dieu, et ils sont demeurés sains et saufs!"
A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
16 Cependant les adorateurs dé l’Eternel s’exhortèrent mutuellement; l’Eternel écouta et entendit, et un registre de souvenir fut dressé devant lui en faveur de ceux qui craignent l’Eternel et qui respectent son nom.
Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
17 Ceux-là seront un trésor pour moi, dit l’Eternel-Cebaot, au jour que je prépare; je les protégerai comme un père protège son fils qui lui est soumis.
“A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
18 De nouveau alors vous verrez la différence du juste au méchant, du serviteur de Dieu à celui qui ne l’aura pas servi.
Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.

< Malachie 3 >