< Lévitique 10 >

1 Les fils d’Aaron, Nadab et Abihou, prenant chacun leur encensoir, y mirent du feu, sur lequel ils jetèrent de l’encens, et apportèrent devant le Seigneur un feu profane sans qu’il le leur eût commandé.
’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2 Et un feu s’élança de devant le Seigneur et les dévora, et ils moururent devant le Seigneur.
Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
3 Moïse dit à Aaron: "C’Est là ce qu’avait déclaré l’Éternel en disant: Je veux être sanctifié par ceux qui m’approchent et glorifié à la face de tout le peuple!" Et Aaron garda le silence.
Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
4 Moïse appela Michaël et Elçafan, fils d’Ouzziel, oncle d’Aaron, et leur dit: "Approchez! Emportez vos frères de devant le sanctuaire, hors du camp."
Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
5 Ils s’avancèrent et les transportèrent dans leurs tuniques hors du camp, selon ce qu’avait dit Moïse.
Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
6 Moïse dit à Aaron, et à Eléazar et Ithamar ses fils: "Ne découvrez point vos têtes et ne déchirez point vos vêtements, si vous ne voulez mourir et attirer la colère divine sur la communauté entière; à vos frères, à toute la maison d’Israël, de pleurer ceux qu’a brûlés le Seigneur.
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
7 Et ne quittez point le seuil de la Tente d’assignation, de peur que vous ne mouriez; car l’huile d’onction du Seigneur est sur vous." Ils se conformèrent à la parole de Moïse.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
8 L’Éternel parla ainsi à Aaron:
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
9 "Tu ne boiras ni vin ni liqueur forte, toi non plus que tes fils, quand vous aurez à entrer dans la Tente d’assignation, afin que vous ne mouriez pas: règle perpétuelle pour vos générations;
“Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
10 et afin de pouvoir distinguer entre le sacré et le profane, entre l’impur et ce qui est pur,
Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
11 et instruire les enfants d’Israël dans toutes les lois que l’Éternel leur a fait transmettre par Moïse."
za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
12 Moïse dit à Aaron ainsi qu’à Eléazar et à Ithamar, ses fils survivants: "Prenez la part d’oblation qui reste des combustions du Seigneur, et mangez-la en pains azymes à côté de l’autel, car elle est éminemment sainte.
Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
13 Vous la mangerez donc en lieu saint, c’est ton droit et celui de tes fils sur les combustions du Seigneur; car ainsi en ai-je reçu l’ordre.
Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
14 Quant à la poitrine qui a été balancée et à la cuisse qui a été prélevée, vous les mangerez en lieu pur, toi ainsi que tes fils et tes filles; car elles ont été assignées comme revenu à toi et à tes enfants, sur les sacrifices rémunératoires des enfants d’Israël.
Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
15 Cette cuisse à prélever et cette poitrine à balancer, ils doivent les joindre aux graisses destinées au feu, pour qu’on en opère le balancement devant le Seigneur; alors elles t’appartiendront, et de même à tes enfants, comme portion invariable, ainsi que l’a statué l’Éternel."
Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
16 Au sujet du bouc expiatoire, Moïse fit des recherches, et il se trouva qu’on l’avait brûlé. Irrité contre Eléazar et Ithamar, les fils d’Aaron demeurés vivants, il dit:
Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
17 "Pourquoi n’avez-vous pas mangé l’expiatoire dans le saint lieu, alors que c’est une sainteté de premier ordre, et qu’on vous l’a donné pour assumer les fautes de la communauté, pour lui obtenir propitiation devant l’Éternel?
“Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
18 Puisque le sang de cette victime n’a pas été introduit dans le sanctuaire intérieur, vous deviez la manger dans le sanctuaire, ainsi que je l’ai prescrit!"
Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
19 Aaron répondit à Moïse: "Certes, aujourd’hui même ils ont offert leur expiatoire et leur holocauste devant le Seigneur, et pareille chose m’est advenue; or, si j’eusse mangé un expiatoire aujourd’hui, est-ce là ce qui plairait à l’Éternel?"
Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
20 Moïse entendit, et il approuva.
Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.

< Lévitique 10 >