< Josué 4 >

1 Comme la nation entière achevait de passer le Jourdain, l’Eternel parla à Josué en ces termes
Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 "Choisissez douze hommes parmi le peuple, un homme par tribu,
“Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
3 et donnez-leur l’ordre d’enlever d’ici, du milieu du Jourdain, à l’endroit même où se sont posés les pieds des prêtres, douze pierres, que vous emporterez pour les déposer dans le gîte où vous passerez la nuit."
ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
4 De son côté, Josué manda les douze hommes qu’il avait fait désigner parmi les enfants d’Israël, un homme par tribu,
Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
5 et il leur dit: "Passez devant l’arche de l’Eternel, votre Dieu, entrez dans le Jourdain, et ramassez-y chacun une pierre qu’il chargera sur son épaule, nombre égal à celui des tribus d’Israël,
ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
6 afin que ce soit un monument au milieu de vous; et lorsqu’un jour vos enfants demanderont: "Que signifient pour vous ces pierres?"
yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
7 Vous leur direz: "C’Est que les eaux du Jourdain se sont séparées devant l’arche d’alliance du Seigneur, qu’à son entrée dans le Jourdain le fleuve divisa ses eaux. Et ces pierres doivent en rappeler à jamais le souvenir aux enfants d’Israël."
Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
8 Les enfants d’Israël se conformèrent à l’ordre de Josué. Ils prirent au milieu du Jourdain, comme l’Eternel l’avait dit à Josué, douze pierres, selon le nombre des tribus d’Israël, les transportèrent au gîte et les y déposèrent.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
9 De son côté, Josué érigea douze pierres dans le Jourdain même, à l’endroit où s’était posé le pied des prêtres portant l’arche d’alliance; et elles y sont restées jusqu’à ce jour.
Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
10 Or, les prêtres portant l’arche étaient restés au milieu du Jourdain, jusqu’à ce que fût accompli tout ce que l’Eternel avait fait dire au peuple par Josué, et selon ce que Moïse avait recommandé à Josué; le peuple passa rapidement.
Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
11 Et lorsqu’il fut entièrement passé, l’arche du Seigneur s’avança avec les prêtres et se remit à la tête du peuple.
Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
12 Les tribus de Ruben et de Gad, et la demi-tribu de Manassé, marchèrent en armes à l’avant-garde des enfants d’Israël, comme Moïse le leur avait dit.
Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
13 Au nombre d’environ quarante mille guerriers, ils s’acheminèrent, prêts au combat, sous les yeux de l’Eternel, vers les plaines de Jéricho.
Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
14 Ce jour-là, l’Eternel grandit Josué aux yeux de tout Israël, qui le révéra comme il avait révéré Moïse, tant qu’il vécut.
A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
15 L’Eternel dit à Josué:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
16 "Ordonne aux prêtres, porteurs de l’arche du Statut, qu’ils remontent du Jourdain."
“Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
17 Et Josué ordonna aux prêtres de sortir du Jourdain.
Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
18 Or, lorsque les prêtres, porteurs de l’arche d’alliance de l’Eternel, eurent quitté le fleuve, à peine la plante de leurs pieds avait touché le sol que les eaux du Jourdain reprirent leur niveau et recommencèrent à couler, comme précédemment, à pleins bords.
Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
19 Ce fut le dix du premier mois que le peuple sortit du Jourdain; il établit son camp à Ghilgal, à l’orient de Jéricho.
A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
20 Et ces douze pierres qu’ils avaient prises dans le Jourdain, c’est à Ghilgal que Josué les érigea,
Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
21 disant aux enfants d’Israël: "Quand vos enfants, un jour, demanderont à leurs pères: "Que signifient ces pierres?"
Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
22 Vous l’expliquerez à vos enfants en ces termes: "Le Jourdain que voici, Israël l’a traversé à pied sec;
Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
23 parce que l’Eternel, votre Dieu, dessécha pour vous les eaux du Jourdain jusqu’à ce que vous fussiez passés, comme il avait fait pour la mer Rouge, qu’il dessécha en notre faveur jusqu’à ce que nous l’eussions traversée:
Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
24 afin que tous les peuples de la terre reconnaissent combien est puissante la main du Seigneur, afin que vous-mêmes révériez constamment l’Eternel, votre Dieu!"
Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”

< Josué 4 >