< Josué 17 >
1 Le lot attribué à la tribu de Manassé, parce qu’il était le premier-né de Joseph, échut à Makhir, premier-né de Manassé, père de Ghilead; et, comme il était belliqueux, il eut le Galaad et le Basan.
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 Les autres descendants de Manassé reçurent selon leurs familles, savoir: les fils d’Abiézer, ceux de Hêlek, ceux d’Asriel, ceux de Sichem, ceux de Héfer et ceux de Chemida, formant la descendance mâle de Manassé, fils de Joseph, selon leurs familles.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 Mais Celofhad, fils de Héfer, fils de Ghilead, fils de Makhir, fils de Manassé, n’avait pas de fils, rien que des filles, lesquelles se nommaient: Mahla, Noa, Hogla, Milca et Tirça.
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 Elles se présentèrent devant le pontife Eléazar, devant Josué, fils de Noun, et les phylarques, en disant: "L’Eternel a ordonné à Moïse de nous attribuer un patrimoine parmi nos frères." Et on leur attribua, selon la parole de l’Eternel, un patrimoine parmi les frères de leur père.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 A Manassé échurent donc dix parts, outre le pays de Galaad et le Basan, situés au delà du Jourdain;
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 car les descendantes de Manassé obtinrent une propriété parmi ses descendants, tandis que le pays de Galaad appartint aux autres descendants de Manassé.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 Or, la limite de Manassé était, en partant d’Aser: Mikhmetat, situé devant Sichem: de là elle s’étendait à droite vers les habitants d’En-Tappouah
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 (Manassé possédait le canton de Tappouah, mais Tappouah même, à la frontière de Manassé, était aux enfants d’Ephraïm).
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 La limite descendait jusqu’au midi du torrent de Kana: les villes de ce côté, enclavées parmi celles de Manassé, appartenaient à Ephraïm, tandis que la limite de Manassé était au nord du torrent et se terminait à la mer.
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 A Ephraïm ce qui était au sud, à Manassé ce qui était au nord, avec la mer pour limite; ils touchaient Aser au nord, Issachar à l’orient.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 Manassé eut encore, dans les cantons d’Issachar et d’Aser, Bethcheân avec ses bourgades, Yibleam avec les siennes, les habitants de Dor et de En-Dor avec leurs dépendances, ceux de Taanakh et de Meghiddo avec les leurs, trois provinces.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 Toutefois, les enfants de Manassé ne purent déposséder la population de ces villes, les Cananéens étant résolus à demeurer dans ce pays.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 Devenus plus forts, les Israélites soumirent les Cananéens à un tribut, mais ne les expulsèrent point.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 Les descendants de Joseph se plaignirent en ces termes à Josué: "Pourquoi nous as-tu donné pour héritage un seul lot et un seul district, alors que nous formons une population nombreuse, tellement l’Eternel nous a bénis?"
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 Josué leur répondit: "Si vous êtes tellement nombreux, montez dans la région boisée, et ouvrez-vous y un passage au pays des Phérézéens et des Rephaïm, puisque la chaîne d’Ephraïm est trop étroite pour vous."
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 "En effet, reprirent les descendants de Joseph, la montagne ne nous suffit point, et, d’autre part, tous les Cananéens de la plaine ont des chariots de fer, ainsi que ceux de Bethcheân et de ses dépendances, et ceux de la vallée de Jézreél."
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 Mais Josué dit à la famille de Joseph, aux tribus d’Ephraïm et de Manassé: "Vous êtes un peuple nombreux, vous êtes pleins d’énergie, vous ne sauriez avoir un lot unique.
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 La montagne doit être à vous! Ce n’est que bois, mais vous la déboiserez, et vous en posséderez jusqu’aux points extrêmes; car vous en chasserez le Cananéen, malgré ses chariots de fer, malgré sa puissance!"
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”