< Josué 16 >

1 Le lot qui échut aux enfants de Joseph partait du Jourdain, près de Jéricho, à l’est des eaux de Jéricho, suivant le désert qui monte de Jéricho, par la montagne, à Béthel;
Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
2 se dirigeait de Béthel à Louz, passait devant la frontière de l’Arkéen à Ataroth;
Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
3 descendait à l’ouest, devant la frontière du Yaflétéen, jusqu’à celle de Béthorôn-le-Bas et jusqu’à Ghézer, et se terminait à la mer.
ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
4 Tel fut l’héritage des enfants de Joseph, Manassé et Ephraïm.
Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
5 Or, la frontière des enfants d’Ephraïm, selon leurs familles, la frontière de leur patrimoine fut: à l’est, Atrot-Addar, jusqu’à Béthorôn-le-Haut;
Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
6 puis elle s’étendait à l’ouest, jusqu’au nord de Mikhmetat: tournait à l’orient de Taanat-Chilo, qu’elle franchissait jusqu’à l’orient de Yanoha;
ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
7 descendait de Yanoha vers Atarot et Naara, atteignait Jéricho et aboutissait au Jourdain.
Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
8 De Tappouah elle allait à l’ouest jusqu’au torrent de Kana et avait pour terme la mer: tel fut le patrimoine des enfants d’Ephraïm selon leurs familles,
Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
9 outre les villes particulières des enfants d’Ephraïm, enclavées, avec leurs dépendances, dans le patrimoine des enfants de Manassé.
Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
10 On n’expulsa point les Cananéens établis à Ghézér; de sorte qu’ils demeurèrent au milieu d’Ephraïm jusqu’à ce jour et furent assujettis à un tribut.
Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.

< Josué 16 >