< Josué 15 >

1 Le lot qui échut à la tribu des enfants de Juda, selon leurs familles, touchait à la frontière d’Edom, près du désert de Cîn au midi, au point extréme de cette région.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 Leur limite méridionale commençait à l’extrémité de la mer Salée, à la pointe qui regarde le sud,
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 se continuait au sud de la montée d’Akrabbîm en passant par Cîn, montait au sud de Kadêch-Barnéa en avant de Héçrôn, de là vers Addar, d’où elle tournait vers Karka;
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 passait par Açmôn, aboutissait au torrent d’Egypte et avait pour limite la mer: "Telle sera pour vous la frontière méridionale."
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 Celle de l’orient est la mer Salée, jusqu’à l’embouchure du Jourdain; celle du côté du nord part de la langue de mer où se termine le Jourdain.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 Cette limite monte vers Beth-Hogla, passe au nord de Beth-Haaraba, monte vers la Pierre de Bohân ben-Ruben;
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 arrive à Debir en partant de la vallée d’Akhor; se dirige, par le nord, vers Ghilgal, en face de la montée d’Adoummîm, au midi du bas-fonds; avance jusqu’aux eaux d’En-Chémech et atteint En-Roghel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 De là, elle monte vers la vallée de Ben-Hinnom, au flanc méridional de Jébus, qui est Jérusalem, court au sommet de la montagne qui regarde, à l’ouest, la vallée de Hinnom, et qui borne, au nord, la vallée de Rephaïm.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 Du sommet de la montagne, la limite s’infléchit vers la source de Mê-Neftoah, se dirige vers les villes de la montagne d’Efrôn, tourne vers Baala, qui est Kiryath-Yearim,
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 passe de Baala à l’ouest, vers le mont Séir, de là, au flanc nord du mont Yearim, qui est Kessalôn, descend vers Beth-Chéméch, de là à Timna;
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 de là, elle gagne le côté nord d’Ekron, s’infléchit vers Chikkerôn, vers la montagne de Baala, vers Yabneêl, et se termine à la mer.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 Pour la limite occidentale, elle est formée par la grande Mer. Telle fut, dans son périmètre, la frontière des enfants de Juda, selon leurs familles.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 Caleb, fils de Yefounné, obtint une part parmi les enfants de Juda, selon la parole de l’Eternel à Josué, savoir la Cité d’Arba, empire des Anakéens, aujourd’hui Hébron.
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 Caleb en expulsa les trois fils d’Anak: Chêchaï, Ahimân et Talmaï, tous enfants d’Anak.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 De là, il s’avança contre les habitants de Debir, laquelle s’appelait autrefois Kiryath-Sêfer.
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 Et Caleb dit: "Celui qui vaincra Kiryath-Sêfer et s’en rendra maître, je lui donnerai ma fille Akhsa pour femme."
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 Othoniel, fils de Kenaz, frère de Caleb, s’empara de la ville, et celui-ci lui donna pour femme sa fille Akhsa.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 En se rendant près de son époux, elle l’excita à demander à son père un certain champ; puis elle descendit de l’âne, et Caleb lui demanda: "Que veux-tu?"
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 Elle répondit: "Fais-moi un présent, car tu m’as reléguée dans une contrée aride; donne-moi donc des sources d’eau!" Et il lui donna les sources supérieures et les sources inférieures.
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 Tel fut le patrimoine de la tribu des enfants de Juda, selon leurs familles.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 Les villes de cette tribu qui se trouvaient à l’extrémité méridionale, vers la frontière d’Edom furent les suivantes: Kabceêl, Eder, Yagour;
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 Kina, Dimona, Adada;
Kina, Dimona, Adada,
23 Kédech, Haçor, Yithnân;
Kedesh, Hazor, Itnan,
24 Ziph, Télem, Bealoth;
Zif, Telem, Beyalot,
25 Haçor-Hadatta, Keriyoth, Héçrôn, autrement Haçor;
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
26 Amâm, Chema, Molada;
Amam, Shema, Molada,
27 Haçor-Gadda, Héchmôn, Beth-Pélet;
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 Haçor-Choual, Bersabée, Bizyothya;
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
29 Baala, Iyyim, Ecem;
Ba’ala, Iyim, Ezem,
30 Eltolad, Kecil, Horma;
Eltolad, Kesil, Horma,
31 Ciklag, Madmanna, Sansanna;
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebaoth, Chilhîm, Ayîn et Rimmôn: ensemble vingt-neuf villes avec leurs dépendances.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 Dans la plaine: Echtaol, Çorea, Achna;
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 Zanoah, En-Gannim, Tappouah, Enam;
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 Yarmouth, Adoullam, Sokho, Azêka;
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 Chaaraïm, Adithaïm, Ghedêra avec Ghedêrothaïm: quatorze villes avec leurs dépendances.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 Cenân, Hadacha, Migdal-Gad
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 Dileân, Miçpé, Yokteêl;
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lakhich, Boçkath, Eglôn;
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 Kabbôn, Lahmâs, Kithlich;
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 Ghedérot, Beth-Dagon, Naama et Makkêda: seize villes avec leurs dépendances.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
42 Libna, Ether, Achân
Libna, Eter, Ashan,
43 Yiphtah, Achna, Necib;
Yefta, Ashna, Nezib,
44 Keïla, Akhzib et Marêcha: neuf villes, outre leurs dépendances.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 Ekron, avec les villes et bourgades qui en dépendent,
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
46 d’Ekron jusqu’à la mer, toutes les villes avoisinant Asdod, avec leurs dépendances;
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
47 Asdod, avec ses villes et ses bourgades; Gaza, avec les siennes, jusqu’au torrent d’Egypte, la grande mer servant de limite.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 Dans la montagne: Chamir, Yathir, Sokho;
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 Danna, Kiryath-Sanna, autrement Debir;
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
50 Anab, Echtemo, Anîm
Anab, Eshtemo, Anim,
51 Gochên, Holôn et Ghilo: onze villes, outre leurs dépendances.
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
52 Arab, Douma, Echeân;
Arab, Duma, Eshan,
53 Yanoum, Beth-Tappouah, Aphêka;
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 Houmta, Kiryath-Arba ou Hébron, et Cior: neuf villes, plus leurs dépendances.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 Maôn, Carmel, Ziph, Youta;
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 Jezreêl, Yokdeâm, Zanoah;
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Kaïn, Ghibea et Timna: dix villes avec leurs dépendances.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 Halhoul, Beth-Çour, Ghedor;
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 Marath, Beth-Anoth et Eltekôn: six villes avec leurs dépendances.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 Kiryath-Baal (la même que Kiryath-Yearim) et Harabba: deux villes, outre leurs dépendances.
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 Dans le désert: Beth ha-Araba, Middïn, Sekhakha;
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 Nibchân, Ir-Hammélah et En-Ghedi: six villes avec leurs dépendances.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 Quant aux Jébuséens, qui habitaient Jérusalem, les enfants de Juda ne purent les déposséder; de sorte qu’ils sont demeurés à Jérusalem, avec les enfants de Juda, jusqu’à ce jour.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.

< Josué 15 >