< Josué 14 >

1 Voici maintenant les possessions des Israélites dans le pays de Canaan, qui leur furent réparties par le prêtre Eléazar et Josué, fils de Noun, assistés des chefs de famille des tribus d’Israël.
Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
2 Cette répartition se fit au sort, comme l’Eternel l’avait ordonné par Moïse, entre les neuf tribus et demie.
Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
3 Car Moïse avait assigné leur patrimoine aux deux autres tribus et demie au delà du Jourdain, mais n’avait pas assigné de terre patrimoniale aux Lévites,
Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
4 d’autant que les fils de Joseph formèrent deux tribus, Manassé et Ephraïm; on ne donna donc point de part aux Lévites dans le pays, si ce n’est certaines villes pour y demeurer, avec les banlieues pour leurs bestiaux et autres biens qu’ils possédaient.
gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
5 Les Israélites procédèrent, dans le partage du pays, selon ce que l’Eternel avait ordonné à Moïse.
Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Les enfants de Juda s’étaient présentés devant Josué à Ghilgal, et Caleb, fils de Yefounné, le Kenizzéen, lui avait dit: "Tu sais ce que l’Eternel a dit à Moïse, l’homme de Dieu, sur mon compte et sur le tien, à Kadêch-Barnéa.
Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
7 J’Étais âgé de quarante ans, lorsque Moïse, serviteur de l’Eternel, m’envoya de Kadêch-Barnéa pour explorer ce pays, et je lui en fis un rapport conforme à ma pensée.
Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
8 Mes frères, qui y étaient allés avec moi, jetèrent le découragement parmi le peuple, mais moi je restai fidèle à l’Eternel, mon Dieu.
amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
9 Ce jour-là, Moïse me fit un serment, en disant: "Assurément, ce pays qu’a foulé ton pied t’appartiendra, comme un patrimoine, à toi et à tes descendants pour toujours, parce que tu es resté fidèle à l’Eternel, mon Dieu.
Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
10 Effectivement, l’Eternel m’a conservé la vie, comme il l’avait annoncé. Voici quarante-cinq ans que l’Eternel adressa cette parole à Moïse, alors qu’Israël voyageait dans le désert, et voici qu’à présent j’ai quatre-vingt-cinq ans.
“Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
11 Robuste encore comme le jour où Moïse me donna cette mission, j’ai la même vigueur aujourd’hui qu’alors, pour la guerre et pour toute expédition.
Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
12 Donne-moi donc cette montagne, que l’Eternel me promit ce jour-là: tu as appris à cette époque que des Anakéens y habitaient, que les villes y sont grandes et fortes; si l’Eternel m’assiste, je les déposséderai, comme l’Eternel l’a dit."
Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
13 Josué bénit Caleb, fils de Yefounné, et lui donna Hébron comme héritage.
Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
14 C’Est pourquoi, Hébron est resté, jusqu’à ce jour, le partage de Caleb, fils de Yefounné, le Kenizzéen, en récompense de sa fidélité à l’Eternel, Dieu d’Israël.
Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
15 Or, le nom primitif de Hébron était: la Cité d’Arba, qui était le plus grand des Anakéens. Et le pays, délivré de la guerre, demeura tranquille.
(Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.

< Josué 14 >