< Job 6 >

1 Job reprit la parole et dit:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Ah! Si seulement on pesait mon chagrin, en mettant en même temps mon malheur dans la balance!
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Assurément, ils seraient plus lourds que le sable des mers; voilà pourquoi mes paroles sont pleines de trouble.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 C’Est que les flèches du Tout-Puissant m’ont transpercé, mon âme en a bu le venin. Les terreurs de Dieu sont rangées en bataille contre moi.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Est-ce que l’âne sauvage se met à braire en présence de l’herbe? Le bœuf mugit-il devant sa pitance?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Peut-on manger un mets insipide sans y mettre du sel? Trouve-t-on quelque saveur au blanc de l’œuf?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 Mon âme refuse d’y goûter; c’est pour moi comme une répugnante nourriture.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Ah! Qui me donnera que ma demande soit agréée et môn espoir réalisé par Dieu?
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 Oui, que Dieu consente à me broyer, qu’il brandisse la main et me mette en pièces!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Il me resterait du moins cette consolation qui me ferait sauter de joie au fort de souffrances sans rémission de n’avoir pas renié les paroles du Très-Haut.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 Quelle est donc ma force pour que je reste dans l’attente? Quelle doit être ma fin pour que je prenne patience?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Ma force est-elle la force des pierres? Ma chair est-elle d’airain?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 N’Est-il pas vrai que je suis privé de tout secours, et que tout espoir de salut m’est arraché?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 A celui qui se consume de chagrin devrait aller la sympathie de ses amis, eût-il même renoncé à la crainte de Dieu.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 Mes amis, à moi, se montrent perfides comme un torrent, comme des cours d’eau pleins à déborder,
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 qui deviennent troubles par l’affluence des glaçons et grossissent par la fonte des neiges:
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 viennent les chaleurs, ils se réduisent à rien; quand le soleil brûle, ils s’évanouissent sur place.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 A cause d’eux, les caravanes se détournent de leur route, s’enfoncent dans le désert et y périssent.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Les caravanes de Têma les cherchent du regard, les convois de Saba y mettent leur espoir.
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 Mais ils sont déçus dans leur confiance; arrivés sur les lieux, ils sont pleins de confusion.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Certes, c’est là ce que vous êtes devenus pour votre ami: à la vue de ma ruine, vous avez eu peur.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Vous ai-je donc dit: "Donnez-moi! Avec un peu de votre bien, gagnez quelqu’un en ma faveur;
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 et délivrez-moi de la main du persécuteur; du pouvoir des tyrans affranchissez-moi!"
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Instruisez-moi, et je garderai le silence; expliquez-moi en quoi j’ai erré.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Qu’elles sont pénétrantes les paroles de la vérité! Mais que prouvent vos arguments à vous?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Prétendez-vous critiquer des mots? Mais dans l’air se dissipent les discours d’un désespéré!
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 L’Orphelin lui-même, vous seriez capables de le prendre comme enjeu, comme vous trafiqueriez de votre ami.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Maintenant donc, daignez vous tourner vers moi: je ne saurais vous mentir en face.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Oui, revenez de grâce, que l’injustice ne s’accomplisse pas; encore une fois, revenez, mon innocence sera manifeste.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Y a-t-il quelque iniquité sur mes lèvres? Mon palais ne sait-il pas discerner ce qui est mal?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?

< Job 6 >