< Job 39 >

1 Connais-tu le temps où enfantent les chamois des roches? Le temps où les biches mettent bas, l’as-tu observé?
“Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
2 Peux-tu compter les mois de leur grossesse? Sais-tu l’heure de leur délivrance?
Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
3 Elles s’accroupissent, émettent leur portée et se débarrassent de leurs douleurs.
Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
4 Leurs petits gagnent en force, grandissent en plein air, ils partent et ne reviennent plus vers elles.
’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
5 Qui a lâché l’onagre en liberté? Qui a dénoué les liens de l’âne sauvage,
“Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
6 à qui j’ai assigné le désert pour demeure et les plaines salées pour habitation?
Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
7 Il se rit du tumulte de la cité, il n’entend pas les cris d’un maître.
Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
8 Il explore les montagnes pour trouver son pâturage et se met en quête, de n’importe quelle verdure.
Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
9 Le buffle consent-il à te servir? Passera-t-il la nuit à ton râtelier?
“Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
10 L’Attacheras-tu au sillon par une corde, ou ira-t-il hersant les vallées derrière toi?
Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
11 Te fieras-tu à lui, parce que grande est sa force? Lui abandonneras-tu le soin de ton travail?
Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
12 Compteras-tu sur lui pour rentrer ton grain, pour recueillir le produit de ton aire?
Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
13 L’Autruche bat joyeusement des ailes: si seulement ses ailes et ses plumes étaient tendrement fidèles!
“Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
14 Car elle abandonne ses œufs à la terre et les laisse chauffer sur le sable,
Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
15 oubliant qu’un pied peut les fouler et la bête des champs les écraser.
ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
16 Elle est dure pour ses petits, comme s’ils lui étaient étrangers: sa peine aura été en pure perte, et elle n’en a pas de regret.
Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
17 C’Est que Dieu lui a refusé la sagesse et ne lui a pas départi de l’intelligence.
Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
18 Mais quand elle se dresse pour prendre son élan, elle défie chevaux et cavaliers.
Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
19 Est-ce toi qui donnes la vigueur au cheval, qui garnis son cou d’une crinière flottante?
“Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
20 Est-ce toi qui le fais bondir comme la sauterelle? L’Éclat de son ébrouement inspire l’effroi.
Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
21 Il creuse le sol et, tout joyeux de sa force, il s’élance vers la mêlée.
Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
22 Il se rit de la crainte, il ne tremble ni ne recule devant l’épée.
Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
23 Sur son dos résonnent le carquois, la lance étincelante et le javelot.
Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
24 D’Impatience et de colère, il dévore l’espace; il ne se possède plus lorsque sonne le clairon.
Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
25 Au coup de trompette, il dit: "Ah!" Et de loin il flaire la bataille, la voix tonnante des chefs et les cris des combattants.
Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
26 Est-ce par un effet de ton intelligence que l’épervier prend son essor et déploie ses ailes vers le Midi?
“Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
27 Est-ce par ton ordre que l’aigle s’élève et va nicher dans les hauteurs?
Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
28 Il fait du rocher sa demeure et se gîte sur la dent des montagnes et les pics escarpés.
Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
29 De là il guette la proie ses regards portent au loin.
Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
30 Ses aiglons se gorgent de sang partout où il y a des cadavres, il est présent.
’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”

< Job 39 >