< Job 34 >
2 Ecoutez, ô sages, mes discours, et vous, hommes instruits, prêtez-moi votre attention.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Car l’oreille apprécie les discours comme le palais déguste la nourriture.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Mettons-nous en quête de ce qui est juste, examinons entre nous ce qui est bon.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Car Job a dit: "Je suis innocent, et Dieu m’a refusé justice.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 En dépit de mon bon droit, je passe pour menteur; cruel est le coup qui m’a frappé, sans que j’aie failli!"
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Y a-t-il un homme comme Job, buvant le blasphème comme de l’eau,
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 faisant cause commune avec les artisans d’iniquité et allant de pair avec les malfaiteurs?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Car il a dit: "L’Homme ne gagne rien à être en bons termes avec Dieu!"
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 C’Est pourquoi, gens d’intelligence, écoutez-moi: loin de Dieu l’iniquité et du Tout-Puissant l’injustice!
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Car il paie chacun selon ses œuvres et lui assigne le sort mérité par sa conduite.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Non, en vérité, Dieu ne commet pas de mal, le Tout-Puissant ne fausse pas la justice.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Qui lui a confié la direction de la terre? Qui a mis tout l’univers entre ses mains?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 S’Il n’avait de pensée que pour lui-même, s’il retirait à lui son esprit et son souffle,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 toutes les créatures périraient du coup, et l’homme retournerait à la poussière.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Or, si tu jouis de ton bon sens, écoute ceci, prête l’oreille au son de mes paroles:
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Celui qui hait la justice pourrait-il régner? Oseras-tu incriminer l’Etre infiniment juste?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Est-il permis de dire au roi: "scélérat!" et aux princes: "criminels!"
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Eh bien! Lui ne prend pas parti pour les grands, et ne favorise pas le riche contre le pauvre, car ils sont tous l’œuvre de sa main.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 En un clin d’œil, ils meurent, et au milieu de la nuit, le peuple s’agite et ils disparaissent; on supprime les puissants, sans qu’une main se lève.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 C’Est que ses yeux sont ouverts sur les voies de l’homme, il observe chacun de ses pas.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Point de ténèbres, point d’ombre si profonde où puissent se cacher les malfaiteurs.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Car Dieu n’a pas besoin de surveiller longuement un homme, pour le faire comparaître en justice.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Il brise les puissants sans long examen et met d’autres à leur place.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 C’Est parce qu’il connaît leurs œuvres, qu’il les renverse de nuit et les écrase.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 En qualité d’impies, il les frappe aux yeux de nombreux spectateurs,
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 les punissant de s’être détournés de lui, d’avoir méconnu toutes ses voies,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 d’avoir fait monter jusqu’à lui les cris du faible, et retentir à ses oreilles la protestation des miséreux.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Et s’il fait l’apaisement, qui le lui reprochera? Quand il cache sa face, qui pourra le voir? II domine et sur les nations et sur les individus,
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 ne voulant pas du règne des hommes pervers, de ceux qui sont un piège pour les peuples.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Se peut-il qu’on dise à Dieu: "J’Ai expié sans être coupable.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Ce qu’il m’est impossible de voir, apprends-le moi toi-même; si j’ai commis des injustices, je ne récidiverai pas?"
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Est-ce sous ton inspiration qu’Il doit rémunérer, parce que tu exprimes ton dédain ou que tu manifestes tes préférences, toi et non moi? Ce que tu sais, expose-le donc.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Les gens sensés me le diront, les hommes sages qui m’écoutent:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 "Job ne discourt pas en connaissance de cause, ses paroles ne sont pas raisonnables.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Mon souhait serait que Job fût éprouvé encore longtemps, à cause de ses réponses dignes d’hommes iniques;
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 car à son péché il ajoute une faute plus grave: il pense triompher au milieu de nous et prodigue ses propos contre Dieu."
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”