< Job 30 >

1 Et maintenant j’excite les moqueries de gens plus jeunes que moi, dont les pères m’inspiraient trop de mépris pour les mettre avec les chiens de mon troupeau.
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 Aussi bien, à quoi m’eût servi le concours de leurs mains? Pour eux il n’y a point de maturité.
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Epuisés par les privations et la faim, ils rôdent dans le désert, lugubre région de désolation et d’horreur,
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 cueillant des plantes sauvages près des arbrisseaux, se nourrissant de la racine des genêts.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 On les chasse du milieu des hommes et on les poursuit de cris comme des voleurs.
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 Ils sont contraints d’habiter dans d’effrayants ravins, dans les excavations du sol et les crevasses des rochers.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 Ils grognent au milieu des buissons et s’entassent sous les broussailles;
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 troupe méprisable, gens sans aveu, ils se voient expulsés du pays!
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Et à présent, ils me chansonnent; je suis pour eux un thème à railleries.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Ils me témoignent leur dégoût, ils s’écartent de moi et ne se privent pas de me cracher à la figure.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 C’Est que Dieu a brisé les rênes que je tenais en mains, et il m’a humilié; ces gens ont secoué le frein que je leur imposais.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 A ma droite se lève une jeunesse insolente, qui fait glisser mes pas et se fraie vers moi ses routes de malheur.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Ils défoncent mon chemin, coopèrent à ma ruine, sans avoir besoin d’assistance.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Ils montent à' l’assaut comme par une large brèche, ils se précipitent au milieu du fracas.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Des terreurs me poursuivent, chassant comme le vent mon honneur; ma prospérité a passé comme un nuage.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 Et maintenant mon âme se fond en moi, les jours de misère m’ont enserré.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 La nuit ronge les os de mon corps, mes nerfs ne jouissent d’aucun repos.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Par l’extrême violence du choc mon vêtement se déforme: elle m’étreint comme l’encolure d’une tunique.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Dieu m’a plongé dans la fange, et j’ai l’air d’être poussière et cendre.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Je crie vers toi, et tu ne me réponds pas; je me tiens là, et tu me regardes fixement.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Tu es devenu inexorable pour moi, tu me combats avec toute la force de ta main.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Tu m’enlèves sur les ailes du vent, tu m’y fais chevaucher, et tu me fais fondre dans la tempête.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Car je sais bien que tu me mènes à la mort, au rendez-vous de tous les vivants.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Mais est-ce qu’on n’étend pas la main quand on s’effondre? Ne crie-t-on pas au secours lorsqu’on succombe au malheur?
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 Moi-même n’ai-je pas pleuré sur les victimes du sort? Mon cœur ne s’est-il point serré à la vue du malheureux?
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 J’Espérais le bien, et le mal a fondu sur moi; j’attendais la lumière, les ténèbres sont venues.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 Mes entrailles bouillonnent sans relâche, les jours de misère m’ont assailli.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Je marche tout noirci et non par le fait du soleil. Je me lève dans l’assemblée et pousse des cris.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 Je suis devenu le frère des chacals, le compagnon des autruches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Ma peau, toute noircie, se détache de moi, et mes os sont brûlés par le feu de la fièvre.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Et ainsi ma harpe s’est changée en instrument de deuil, et ma flûte émet des sanglots.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >