< Jérémie 52 >

1 Sédécias avait vingt-et-un ans lors de son avènement, et il règna onze ans à Jérusalem; le nom de sa mère était Hamoutal, fille de Jérémie de Libna.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
2 Il fit ce qui est mal aux yeux de l’Eternel, tout comme avait agi Joïakim.
Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
3 C’Est ainsi que la colère de Dieu se manifesta contre Jérusalem et Juda, jusqu’à ce qu’il les eût rejetés de devant sa face. Or. Sédécias entra en révolte contre le roi de Babylone.
Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
4 Alors, dans la neuvième année de son règne, le dixième mois et le dixième jour du mois, Nabuchodonosor, roi de Babylone, marcha avec toute son armée contre Jérusalem; ils campèrent sous ses murs et élevèrent des retranchements sur toute son enceinte.
A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
5 La ville subit le siège jusqu’à la onzième année du règne de Sédécias.
An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
6 Le quatrième mois, le neuvième jour du mois, la famine sévit dans la ville et les gens du peuple manquèrent de pain.
A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
7 Alors la ville fut ouverte par une brèche. Aussitôt tous les gens de guerre s’enfuirent en quittant la ville nuitamment par la porte du double rempart, attenante au parc du roi, tandis que les Chaldéens cernaient la ville, et ils prirent la direction de la Plaine.
Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
8 L’Armée chaldéenne se mit à la poursuite du roi, et elle atteignit Sédécias dans la plaine de Jéricho, alors que sa propre armée s’était débandée en l’abandonnant.
Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
9 On fit le roi prisonnier et on l’amena au roi de Babylone à Ribla dans le district de Hamat, et celui-ci prononça sa sentence.
Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
10 Le roi de Babylone fit égorger les fils de Sédécias sous ses yeux; il fit aussi égorger tous les notables de Juda à Ribla.
Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
11 Puis il fit crever les yeux à Sédécias et le chargea de chaînes. Enfin le roi de Babylone le déporta à Babylone, où il l’enferma dans la maison de détention jusqu’au jour de sa mort.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
12 Le dixième jour du cinquième mois, qui correspond à la dix-neuvième année du règne de Nabuchodonosor, roi de Babylone, Nebouzaradan, chef des gardes, serviteur du roi de Babylone, entra dans Jérusalem.
A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
13 Il mit le feu au temple du Seigneur et au palais du roi; de même il livra aux flammes toutes les maisons de Jérusalem, à savoir toute maison d’un personnage important.
Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
14 Et tous les remparts qui entouraient Jérusalem furent démolis par l’armée chaldéenne, placée sous les ordres du chef des gardes.
Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
15 Une partie de la basse classe et le reste de la population qui était demeurée dans la ville, les transfuges qui s’étaient rendus au roi de Babylone et le surplus de la multitude furent envoyés en exil par Nebouzaradan, chef des gardes.
Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
16 Le chef des gardes, Nebouzaradan, ne laissa dans le pays que des gens de la classe inférieure comme vignerons et laboureurs.
Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
17 Les colonnes d’airain qui se trouvaient dans la maison de Dieu, les supports et la Mer d’airain du temple, les Chaldéens les mirent en pièces et en emportèrent l’airain à Babylone.
Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
18 Ils prirent aussi les cendriers, les pelles, les couteaux, les bassins, les cuillers et tous les ustensiles d’airain qui servaient au culte.
Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
19 Le chef des gardes s’empara encore des marmites, des brasiers; des bassins, des poêles, des chandeliers, des écuelles et des tasses tant en or qu’en argent.
Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
20 Quant aux deux colonnes, à la Mer unique, aux douze boeufs en airain placés sous les supports que le roi Salomon avait faits pour le temple du Seigneur, le poids de l’airain de tous ces objets ne peut être évalué.
Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
21 Chacune des colonnes avait dix-huit coudées de haut, un fil de douze coudées en mesurait le tour, et ses parois avaient une épaisseur de quatre doigts; l’intérieur était creux.
Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
22 Elle était surmontée d’un chapiteau d’airain; chaque chapiteau était haut de cinq coudées. Un treillage et des grenades entouraient le chapiteau, le tout fait d’airain. Il en était de même de la seconde colonne, également garnie de grenades.
A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
23 Les grenades qui apparaissaient sur le côté étaient au nombre de quatre-vingt seize; en réalité, le total des grenades qui entouraient le treillage s’élevait à cent.
Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
24 Le chef des gardes s’assura de la personne de Seraïa, le grand-prêtre, de Cefania, le grand-prêtre suppléant, et des trois gardiens du seuil.
Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
25 Parmi les habitants de la ville, il arrêta un officier, préposé aux gens de guerre, sept des conseillers intimes du roi qui furent surpris dans la ville, le secrétaire, chef du recrutement, chargé d’enrôler la population du pays, ainsi que soixante hommes de cette population, qui se trouvaient dans la ville.
Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
26 Nebouzaradan, chef des gardes, emmena tous ces prisonniers et les conduisit au roi de Babylone à Ribla.
Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
27 Le roi de Babylone les fit frapper et mettre à mort à Ribla. dans le district de Hamat, C’Est ainsi que Juda fut exilé de son territoire.
Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
28 Voici le chiffre de la population que Nabuchodonosor emmena en exil dans la septième année de son règne trois mille vingt-trois Judéens;
Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
29 dans la dix-huitième année du règne de Nabuchodonosor, il emmena de Jérusalem huit cent trente-deux personnes;
a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
30 dans la vingt-troisième année du règne de Nabuchodonosor, Nebouzaradan, chef des gardes, envoya en captivité sept cent quarante cinq Judéens: ce qui donne un total de quatre mille six cents hommes.
a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
31 La trente-septième année de l’exil de Joïachin, roi de Juda, le douzième mois et le vingt-cinquième jour du mois, Evil-Merodac, roi de Babylone, gracia Joïachin, roi de Juda, et le fit sortir de la maison de détention.
A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
32 Il lui parla avec bonté, et lui donna un siège placé au-dessus du siège des rois qui étaient avec lui à Babylone.
Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
33 Il lui fit changer ses vêtements de détention et l’admit constamment à sa table, toute sa vie durant.
Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
34 Son entretien, entretien permanent, lui fut assuré tant qu’il vécut de la part du roi de Babylone, suivant les besoins de chaque jour, jusqu’au moment de sa mort.
Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.

< Jérémie 52 >