< Jérémie 51 >

1 Ainsi parle l’Eternel: "Voici, je vais susciter contre Babel et contre les habitants de la Chaldée un vent destructeur.
Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
2 Je lancerai sur Babel des barbares pour la secouer comme dans un van et faire le vide dans son territoire. Oui, au jour du malheur, ils la cerneront de toutes parts.
Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
3 Que l’archer ne bande pas son arc, qu’il ne revête pas sa cuirasse! Quant-à vous, n’épargnez pas ses jeunes gens, exterminez toute son armée.
Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
4 Qu’ils tombent sur la terre des Chaldéens, frappés à mort, et dans ses rues, transpercés par l’épée!
Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
5 Certes, Israël non plus que Juda n’est veuf de son Dieu, l’Eternel-Cebaot, tandis que le pays des Chaldéens déborde de crimes à l’égard du Saint d’Israël.
Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
6 Fuyez, sortez de Babel, sauvez-vous tous, afin de ne pas périr pour son crime, car c’est un temps de représailles pour l’Eternel, qui lui paie le prix de ses actes.
“Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
7 Babel était entre les mains du Seigneur une coupe d’or, destinée à donner l’ivresse à toute la terre; les nations buvaient de son vin et pour cela entraient en délire.
Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
8 Soudain Babel est tombée, et elle s’est brisée. Pleurez sur elle, cherchez du baume pour ses maux, peut-être guérira-t-elle.
Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
9 Nous avons voulu guérir Babel, mais elle est inguérissable. Abandonnez-la! Que chacun de nous retourne en son pays, puisque son châtiment atteint jusqu’au ciel et s’élève jusqu’à la voûte du firmament!
“‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
10 Le Seigneur a fait éclater notre droit: Allons raconter dans Sion l’oeuvre de l’Eternel, notre Dieu.
“‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
11 Fourbissez les flèches, emplissez les carquois! Le Seigneur a stimulé le courage des rois de Médie, car sa pensée est dirigée contre Babel, dont il veut la destruction: ce sont les représailles de l’Eternel, la revanche de son sanctuaire.
“Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
12 Arborez une bannière près des remparts de Babel, renforcez le poste d’observation, placez des sentinelles, disposez des embuscades, car l’Eternel, il a conçu un dessein et il va exécuter ce qu’il a annoncé contre les habitants de Babel.
Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
13 O toi, qui es assise le long des eaux abondantes, si riche en trésors, ta fin est venue, la mesure de tes rapines est comble.
Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
14 L’Eternel-Cebaot l’a juré par lui-même: Certes, je t’inonderai d’hommes nombreux comme les sauterelles, et ils pousseront contre toi le cri de victoire."
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
15 Il a créé la terre par sa puissance, affermi le monde par sa sagesse, déployé les cieux par son intelligence.
“Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
16 Lorsqu’il fait entendre le bruit du tonnerre, des torrents d’eau s’amassent au ciel; il élève les nuées du bout de la terre, il accompagne d’éclairs la pluie et fait s’échapper le vent de ses réservoirs.
Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
17 Tout être humain est éperdu, incapable de comprendre; tout orfèvre a honte de son idole, car sa statue de fonte est un mensonge, nul souffle de vie en tous ces dieux.
“Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
18 Ce sont des néants, des oeuvres d’aberration; au jour du règlement des comptes, ils périront.
Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
19 Tel n’est point Celui qui est le lot de Jacob; c’est le créateur de l’univers, et Israël est la tribu qui lui appartient en propre: Eternel-Cebaot est son nom.
Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
20 Tu étais pour moi une massue, une arme de guerre; avec toi je broyais les nations, avec toi je détruisais les royaumes.
“Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
21 Avec toi j’écrasais le cheval et son cavalier; avec toi j’écrasais le char et celui qui le montait.
da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
22 Avec toi j’écrasais hommes et femmes, avec toi j’écrasais vieillards et enfants, avec toi j’écrasais jeune homme et vierge.
da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
23 Avec toi j’écrasais le berger et son troupeau, avec toi j’écrasais le laboureur et son attelage, avec toi j’écrasais satrapes et gouverneurs.
da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
24 Mais je rendrai à Babel et à tous les habitants de la Chaldée tout le mal qu’ils ont fait à Sion, je le leur rendrai sous vos yeux, dit le Seigneur.
“Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
25 Voici, c’est à toi que j’en ai, ô montagne de destruction, dit le Seigneur, toi qui as causé la ruine de toute la terre. J’Étendrai ma main contre toi, je te ferai rouler du haut des rochers et te changerai en un mont calciné.
“Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
26 On ne tirera de toi ni pierre d’angle ni pierre de fondation; mais tu seras réduite à l’état de ruine éternelle, dit le Seigneur.
Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
27 Dressez un signal dans le pays, faites résonner le clairon parmi les nations; contre elle, convoquez des peuples, rassemblez les royaumes d’Ararat, de Minni et d’Achkenaz, recrutez des officiers, amenez des chevaux comme une volée de sauterelles aux ailes hérissées.
“Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
28 Convoquez contre elle des peuples, les rois de Médie, Ses gouverneurs et tous ses chefs, et tout le territoire de sa suzeraineté.
Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
29 La terre a frémi et tremblé, car ils s’accomplissent sur Babel, les desseins de l’Eternel, qui veut faire de Babel une solitude inhabitée.
Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
30 Les guerriers de Babel renoncent à combattre, se tiennent cois dans les forts; leur courage s’est évanoui, ils ressemblent à des femmes. On a mis le feu à ses demeures, ses verrous sont brisés.
Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
31 Courrier sur courrier, messager sur messager se précipitent pour annoncer au roi de Babel que sa ville est envahie de toutes parts,
Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
32 que les passages sont occupés, que les fascines sont consumées par le feu, et que les gens de guerre sont dans l’épouvante.
An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
33 Oui, ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: "Babel ressemble à une aire, au temps où elle est piétinée; encore un peu et l’heure de la moisson arrivera pour elle.
Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
34 "II m’avait dépouillée dit Sion, il m’avait affolée, Nabuchodonosor, roi de Babel; il m’avait laissée là comme un vase vidé, après m’avoir avalée comme un dragon et s’être bourré le ventre de mes délices; il m’avait pourchassée.
“Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
35 Que les violences que j’ai subies dans ma chair soient imputées à Babel! s’écrie l’habitante de Sion; que mon sang retombe sur les gens de Chaldée! s’écrie Jérusalem.
Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
36 C’Est pourquoi, ainsi parle le Seigneur, je vais épouser ta querelle et assouvir ta vengeance; je vais dessécher ses eaux et tarir sa source.
Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
37 Et Babel deviendra un monceau de ruines, un repaire de chacals, un objet de stupeur et de raillerie, un lieu inhabité.
Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
38 Ensemble, ils hurleront comme des léopards, ils grinceront comme de jeunes lionceaux.
Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
39 Au plus fort de leur ardeur, je leur présenterai un festin et leur donnerai l’ivresse, pour qu’ils entrent en délire et s’endorment d’un sommeil éternel, pour ne plus se réveiller, dit le Seigneur.
Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
40 Je les traînerai à la boucherie comme des brebis, comme des béliers et des boucs.
“Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
41 Ah! comme Sésac est emportée de force! Comme elle est prise, elle, l’ornement de toute la terre! Comme Babel est devenue une solitude parmi les nations!
“Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
42 La mer s’est élancée sur Babel, de la masse de ses flots elle est recouverte.
Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
43 Ses villes se sont changées en solitude, en une région aride et déserte, où nul homme ne s’établira, que ne traversera nul mortel.
Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
44 Je sévirai sur Bel à Babel, je lui arracherai de la bouche le morceau déjà avalé. Les nations n’y afflueront plus et les murs même. de Babel vont s’écrouler.
Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
45 Partez de là, mon peuple; que chacun sauve sa vie devant l’ardente colère de l’Eternel!
“Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
46 Que votre coeur ne défaille pas! Ne vous effrayez pas des bruits qui se répandent sur la terre cette année, c’est un bruit, l’année prochaine, ce sera un autre bruit. La violence règne sur la terre, potentats contre potentats.
Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
47 Oui, des jours vont venir, où je sévirai contre les idoles de Babel, et tout ce pays sera dans la confusion, et tous ses morts seront couchés sur son sol.
Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
48 Ciel et terre, et tout ce qu’ils renferment, célèbreront la chute de Babel, car c’est du Nord que l’assailleront les dévastateurs, dit l’Eternel.
Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
49 II faut que Babel tombe à son tour, ô victimes d’Israël! puisqu’aussi bien à cause de. Babel sont tombées les victimes de toute la terre.
“Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
50 Vous qui avez échappé au glaive, partez, ne vous arrêtez point! Songez de loin à l’Eternel; que Jérusalem soit présente à votre pensée!
Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
51 "Nous rougissions des outrages que nous étions obligés d’entendre, la honte couvrait notre visage, puisque des étrangers ont envahi les sanctuaires de la maison du Seigneur."
“Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
52 Aussi des jours viendront, dit l’Eternel, où je sévirai sur ses idoles, et où, sur tout son territoire, geindront des. hommes blessés à mort.
“Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
53 Dût Babel monter jusqu’au ciel, ériger dans les hauteurs ses puissantes forteresses, il lui viendrait des dévastateurs suscités par moi, dit l’Eternel.
Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
54 Des cris retentissants montent de Babel, le fracas d’une grande chute du pays des Chaldéens.
“Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
55 Car l’Eternel ravage Babel, il y fait taire cette vaste rumeur qui s’élève lorsque mugissent ses vagues comme des eaux profondes, lorsque se répandent les éclats de sa voix.
Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
56 Oui, le dévastateur se jette sur cette ville, sur Babel, ses guerriers sont pris, leurs arcs sont brisés, car l’Eternel est un Dieu de représailles, il paie sans faute.
Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
57 Je verserai l’ivresse à ses princes et à ses sages, à ses gouverneurs, à ses officiers et à ses guerriers: ils s’endormiront d’un sommeil éternel, pour ne plus se réveiller, dit le Roi, dont le nom est Eternel-Cebaot.
Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
58 Ainsi parle l’Eternel-Cebaot: "Les murs de la grande Babel s’écrouleront de fond en comble, ses portes, si hautes, deviendront la proie des flammes. Voilà comme les peuples travaillent pour le néant et les nations s’exténuent au profit du feu!"
Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
59 Recommandation que fit le prophète Jérémie à Seraïa, fils de Nêria, fils de Mahséia, lorsqu’il se rendit à Babylone sur l’ordre de Sédécias, roi de Juda, dans la quatrième année de son règne; Seraïa était commandant des étapes.
Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
60 Jérémie avait consigné dans un livre toutes les calamités qui devaient atteindre Babylone, tous ces discours qui avaient été rédigés au sujet de cette ville.
Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
61 Jérémie dit donc à Seraïa: "Quand tu arriveras à Babylone, tu auras soin de donner lecture de tous ces discours.
Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
62 Ensuite tu diras: "Eternel! C’Est toi qui as décrété contre cette ville sa complète destruction, au point que nul n’y habitera plus, ni hommes, ni bêtes, et qu’elle se trouvera réduite à l’état de ruine éternelle!"
Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
63 Et lorsque tu auras fini de donner lecture de ce livre, tu y attacheras une pierre et tu le lanceras en plein Euphrate,
Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
64 tout en disant ces mots: "Ainsi s’effondrera Babel, pour ne plus se relever, par l’effet de la calamité que je fais fondre sur elle: ils périront d’épuisement!" Ici se terminent les discours de Jérémie.
Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.

< Jérémie 51 >