< Jérémie 41 >

1 Dans le septième mois, Ismaël, fils de Netania, fils d’Elichama, qui était de race royale et un des hauts dignitaires du roi, arriva, accompagné de dix hommes, auprès de Ghedalia, fils d’Ahikam, à Miçpa; et là, à Miçpa, ils prirent part ensemble à un festin.
A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
2 Puis Ismaël, fils de Netania, et les dix hommes qui étaient avec lui se levèrent, frappèrent par le glaive Ghedalia, fils d’Ahikam, fils de Chafan, et le firent périr, lui que le roi de Babylone avait nommé gouverneur du pays.
sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
3 De même tous les Judéens qui entouraient Ghedalia à Miçpa, ainsi que les Chaldéens qui s’y trouvaientles gens de guerre, Ismaël les massacra.
Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
4 Le second jour, après le meurtre de Ghedalia, que personne encore ne connaissait,
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5 des hommes arrivèrent de Sichem, de Silo et de Samarie, au nombre de quatre-vingts, ayant la barbe rasée, les vêtements déchirés et le corps tailladé, portant dans leurs mains des offrandes et de l’encens qu’ils destinaient au temple de l’Eternel.
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
6 lsmaël, fils de Netania, sortit de Miçpa pour aller à leur rencontre, en pleurant tout le long de la marche, et quand il fut auprès d’eux, il leur dit: "Venez trouver Ghedalia, fils d’Ahikam."
Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
7 Mais dès qu’ils eurent pénétré dans l’intérieur de la ville, Ismaël, aidé des hommes qui étaient avec lui, les égorga et les jeta dans une citerne.
Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
8 Parmi eux se trouvaient dix hommes qui dirent à Ismaël: "Ne nous fais pas mourir, car nous possédons des provisions cachées dans les champs, du froment, de l’orge, de l’huile et du miel." Il les épargna et ne les tua point comme leurs frères.
Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
9 Or, la citerne où Ismaël avait jeté les corps de tous les hommes qu’il avait frappés en même temps que Ghedalia, était celle que le roi Asa avait construite pour se défendre contre Baasa, roi d’Israël; c’est cette citerne qu’Ismaël, fils de Netania, remplit de cadavres.
To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
10 Et Ismaël fit main basse sur tout le reste de la population qui était à Miçpa, sur les princesses royales et l’ensemble des gens qui demeuraient a Miçpa et que Nebouzaradan, chef des gardes, avait placés sous l’autorité de Ghedalia, fils d’Ahikam. Ismaël, fils de Netania, les emmena tous comme prisonniers, et partit pour se rendre chez les Ammonites.
Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
11 Mais Johanan, fils de Karéah, et tous les commandants de troupes qui l’accompagnaient, ayant appris tout le mal fait par Ismaël, fils de Netania,
Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
12 ramassèrent tous leurs hommes, se mirent en route pour attaquer Ismaël, fils de Netania, et l’atteignirent près des grands étangs de Gabaon.
sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
13 Quand tout le peuple qui se trouvait avec Ismaël aperçut Johanan, fils de Karéah, et tous les commandants de troupes qui l’accompagnaient, il fut dans la joie.
Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
14 Et tous les gens qu’Ismaël avait emmenés comme prisonniers de Miçpa firent volte face et, ayant changé de direction, se rallièrent à Johanan, fils de Karéah.
Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
15 Quant à Ismaël, fils de Netania, il se sauva avec huit hommes devant Johanan et se rendit auprès des Ammonites.
Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
16 Puis Johanan, fils de Karéah, et tous les chefs de troupes qui l’accompagnaient prirent tout le restant de la population qu’Ismaël, fils de Netania, avait enlevée de, Miçpa, après avoir assassiné Ghedalia, fils d’Ahikam: les adultes combattants, les femmes, les enfants et les eunuques qu’ils avaient ramenés de Gabaon.
Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
17 Ils se mirent en route et firent halte dans le cantonnement de Kimham, près de Bethléem, dans l’intention de partir de là et de se rendre en Egypte,
Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
18 à cause des Chaldéens, dont ils avaient peur, parce qu’Ismaël, fils de Netania, avait mis à mort Ghedalia, fils d’Ahikam, établi comme gouverneur du pays par le roi de Babylone.
don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.

< Jérémie 41 >