< Jérémie 14 >
1 Voici en quels termes la parole de Dieu fut adressée à Jérémie au sujet de la sécheresse:
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
2 Juda est en deuil, ceux que renferment ses portes sont consternés, tristement assis à terre, et ce sont des cris plaintifs qui s’élèvent de Jérusalem.
“Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
3 Leurs chefs envoient les subalternes chercher de l’eau; ceux-ci arrivent aux citernes, et n’y trouvent pas d’eau; ils reviennent sur leurs pas avec leurs vases vides, pleins de confusion, tout honteux et la tête voilée.
Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
4 C’Est que le sol est crevassé, nulle pluie n’étant tombée dans le pays; les laboureurs sont cruellement déçus et se couvrent la tête d’un voile.
Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
5 Oui, jusqu’à la biche dans les champs qui, après avoir mis bas, abandonne son petit; car il n’y a pas de verdure.
Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
6 Les onagres s’arrêtent sur les hauteurs dénudées, aspirant l’air comme les monstres marins: leurs yeux se consument, car il n’y a pas d’herbe.
Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
7 Si nos fautes nous accusent, ô Eternel, agis pour l’honneur de ton nom, quoique nombreuses soient nos défections et nos prévarications envers toi.
Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
8 Espoir d’Israël, son sauveur au temps de la détresse, pourquoi serais-tu comme un étranger dans le pays, comme un voyageur qui dresse sa tente pour une nuit?
Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
9 Pourquoi serais-tu comme un homme déconcerté, comme un guerrier impuissant à secourir? Tu es pourtant au milieu de nous, ô Eternel, ton nom est associé au nôtre, tu ne peux nous abandonner.
Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
10 Ainsi parle l’Eternel au sujet de ce peuple: "En vérité, il leur plaisait d’aller de côté et d’autre, sans ménager leurs pas; mais Dieu ne les a pas vus avec plaisir. A présent il se souvient de leurs fautes, il leur demande compte de leurs péchés."
Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
11 L’Eternel me dit encore: "Ne prie pas pour ce peuple, pour son bonheur.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
12 S’Il jeûne, je resterai sourd à ses supplications; s’il m’offre des holocaustes et des oblations, je ne leur ferai pas bon accueil. Bien plus, par le glaive, par la famine et la peste, je vais le faire périr."
Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
13 Je m’écriai: "Eh quoi! ô Eternel, Dieu, mais des prophètes leur disent: Vous ne verrez pas de glaive, la famine ne sévira point parmi vous; c’est, au contraire, une paix durable que je vous octroie en ces lieux!"
Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
14 L’Eternel me répondit: "Ce sont des mensonges que ces prophètes prophétisent en mon nom! Je ne les ai point envoyés, je ne les ai chargés d’aucune mission, ni ne leur ai parlé: ce sont des visions imaginaires, des prédictions vaines, des tromperies forgées par leur coeur qu’ils vous prophétisent."
Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
15 C’Est pourquoi ainsi parle l’Eternel: "Pour ce qui est des prophètes qui prophétisent en mon nom, alors que je ne les ai point envoyés, et qui disent que ni glaive ni famine ne séviront en ce pays, eh bien! Par le glaive et la famine ils périront, ces prophètes!
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
16 Et ce peuple auquel s’adressent leurs prophéties, il jonchera les rues de Jérusalem, victime du glaive et de la famine; personne ne les ensevelira, ceux-là, ni eux, ni leurs femmes, ni leurs fils, ni leurs filles; je ferai retomber sur eux leur impiété.
Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
17 Et toi, tu leur adresseras cette parole: Nuit et jour mes yeux fondent en Larmes, sans discontinuer, car la vierge, fille de mon peuple, est atteinte d’une terrible catastrophe, d’une blessure douloureuse à l’extrême.
“Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
18 Si je sors dans les champs, voilà ceux qui sont tombés victimes du glaive; si j’entre dans la ville, voici ceux que torture la faim; oui, tant prophètes que prêtres, ils errent sans but dans le pays."
In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
19 As-tu donc complètement repoussé Juda? Ton âme a-t-elle pris Sion en dégoût? Pourquoi nous infliges-tu des blessures auxquelles il n’est point de remède? On espérait la paix et rien d’heureux ne nous arrive, une ère de réparation et voici l’épouvante!
Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
20 Nous reconnaissons, ô Seigneur, notre culpabilité, la faute de nos ancêtres; assurément, nous avons péché contre toi.
Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
21 Pour l’honneur de ton nom ne livre pas au mépris, n’avilis point ton trône glorieux; souviens-toi, ne romps pas ton alliance avec nous.
Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
22 En est-il parmi les vaines divinités des nations qui répandent la pluie? Ou bien est-ce le ciel qui dispense les ondées? N’Est-ce point toi, ô Eternel, notre Dieu, toi en qui nous mettons notre espoir? Oui, toi, tu accomplis tous ces prodiges.
Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.