< Isaïe 4 >

1 En ce jour, sept femmes s’attacheront à un seul homme et lui diront: "Nous voulons subvenir nous-mêmes à notre nourriture et pourvoir à nos vêtements, donne-nous seulement ton nom, mets fin à notre déshonneur."
A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
2 En ce jour, la plante du Seigneur sera revêtue d’éclat et de splendeur, et le fruit du pays fera l’orgueil et la gloire des débris d’Israël,
A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
3 et on dénommera saint quiconque aura été sauvé dans Sion et épargné dans Jérusalem, quiconque aura été marqué pour la vie à Jérusalem.
Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
4 Une fois que le Seigneur aura lavé la souillure des filles de Sion et nettoyé Jérusalem du sang qui la tache, en y faisant passer un souffle de justice, un vent de destruction,
Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
5 alors l’Eternel créera sur toute l’étendue de la montagne de Sion et de ses lieux d’assemblée une nuée et une vapeur pendant le jour et, pendant la nuit, l’éclat d’un feu flamboyant; oui, tout endroit vénéré sera abrité par un dais.
Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
6 Il y aura comme une tente donnant, le long du jour, de l’ombre contre la chaleur, servant d’asile et de refuge contre l’orage et la pluie.
Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.

< Isaïe 4 >